Jagora: Iran Tana Fuskantar Makiya Na Waje Kafirar Da Munafikai
Published: 3rd, March 2025 GMT
Jagoran juyin juya halin musulunci na Iran Ayatullah Sayyid Ali Khamnei ya bayyana cewa; al’ummar Iran tana fuskantar makiya kafirai da munafikai, amma kasar ba ta da matsala da sauran al’ummun duniya.
Har ila yau jagoran ya ce, alkur’ani mai girma yana kunshe da hanyoyin da ya kamata a yi mu’amala da dukkanin wadannan makiyan, da kuma lokacin da ya kamata a yi Magana da su, ko kuma lokacin da ya kamata a zare musu takobi.
Ayatullah Sayyid Ali Khamnei wanda ya gabatar da jawabi a wurin taron karatun alkur’ani mai girma, a jiya Lahadi da dare, ya yi ishara da cutukan ruhi da su ka addabi bil’adama a wannan zamanin da su ka hada hassada, rowa,mummunan zato, ganda da son kai, da kuma fifita manufa ta kashin kai akan ta al’umma, tare da bayyana cewa, a cikin alkur’ani mai girma da akwai magungunan dukkanin wadannan cutukan.
Jagoran juyin musuluncin ya kuma ce, a bisa mahanga ta musulunci abu na biyu mai muhimmanci bayan tauhidi da ilimi da kyautata alaka da Allah, shi ne shimfida adalci a cikin al’ummar musulmi.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Sun Rage Zuwa Kasashen Waje
Lamarin ya ci gaba da raguwa har zuwa 2024, inda yawan kudaden da ake kashewa a yawon ketare ya fadi da kaso 14 a matakin shekara-shekara zuwa dala biliyan 2.66.
Hakan na nuni da cewa ‘yan Nijeriya sun rage kashe kudaden da suke kashewa kan safarar jiragen sama da dala biliyan 1.12 ko kuma kashi 30 cikin dari a cikin shekaru biyun.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp