Hukumar wayar da kan jama’a ta kasa NOA, ta yi kira ga al’ummar Musulmi da su yi amfani da wannan lokaci na watan Ramadan wajen tunanin abubuwan da za su amfani kasa baki daya.

Kodinetan hukumar na jihar Jigawa Mallam Ahmed Tijjani Ibrahim
ya yi wannan kiran a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Dutse, babban birnin jihar.

Malam Ahmed Tijjani ya kuma yi kira ga al’ummar Musulmi da su yi addu’ar zaman lafiya, da tsaro da ci gaban jihar da kasa baki daya.

Ya bayyana watan Ramadan a matsayin wata mai alfarma da ake son musulmi su kara kusanta ga  Allah SWT, ta hanyar tsarkake zukatansu.

Don haka Tijjani ya umarce su da su zama ’yan uwan juna, su kasance masu hakuri da kamun kai, da tausaya wa marasa galihu a cikin al’umma.

Ya kara da cewa, NOA za ta bi sahun gwamnatin jihar domin sanya ido da kuma lura da al’amuran da ke gudana a watan Ramadan na wannan shekara domin tabbatar da ganin komi ya tafi yadda ake bukata.

 

Usman Muhammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Ramadan

এছাড়াও পড়ুন:

Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Afirka Sun Yi Alkawarin Karfafa Alaka

Da yake nasa jawabin, Sangare ya ce, Nijar na bin manufar Sin daya tak a duniya, kuma tana ba da fifiko ga hadin gwiwarta da kasar Sin, da mayar da hankali sosai kan harkokin tsaro, kana tana son kara amincewa da juna, da ci gaba da yin shawarwari bisa mutunta juna a tsakaninsu. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAF Na Shirin Siyo Jiragen Yaki Masu Saukar Ungulu Daga Amurka
  • An samu gobara a wasu matatun mai guda biyu na Iran bayan harin da Isra’ila ta kai
  • Gwamnan Kaduna ya bai wa sabon Sarkin Moro’a sandar mulki
  • Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi
  • Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya
  • Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Gina Kasa A Gabar Da Ake Bikin Cika Shekaru 120 Da Haihuwar Dan Mazan Jiya Chen Yun
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • Bukatar Kara Yawan Masu Fitowa Kada Kuri’a A Zabuka Nan Gaba
  • Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Afirka Sun Yi Alkawarin Karfafa Alaka
  • ICPC Ta Gurfanar Da Ma’aikacin Kotu Bisa Badakalar Naira Miliyan 9.2