Leadership News Hausa:
2025-04-30@19:42:44 GMT

Rashin Tsaro A Nijeriya: Gazawar Masu Mulki Ce Da Cin Amanar Kasa

Published: 2nd, February 2025 GMT

Rashin Tsaro A Nijeriya: Gazawar Masu Mulki Ce Da Cin Amanar Kasa

A cewar wani rahoto da kamfanin nazarin al’amuran yau da kullun da siyasa a Najeriya (SBM Intelligence) ya gabatar, tsakanin shekara ta 2011 zuwa 2020, an biya akalla dala miliyan 18.34, wanda ya yi daidai da Naira biliyan 23; ga masu garkuwa da mutane a matsayin kudin fansa.

Ko shakka babu, garkuwa da mutane ya fi aikin gwamnati ko siyasa riba.

Sannan, shin su wa ke amfani da kudaden fansar da ake biya ga masu garkuwa da mutanen? Hasashe ya nuna cewa, mai yiwuwa a yi amfani da kudaden don kara sayen bindigogi da sauran makamantansu.

 

Tambayoyin Da Ke Bukatar Amsa Da Matsalolin Da Ke Bukatar Warwarewa

A cikin wannan rudani, ka da mu manta da irin yadda gwamnati ta yi biris da kokarin ganin an magance matsalar rashin tsaron da ke addabar al’ummar wannan kasa, tun daga bangaren zartarwa zuwa na majalisa da kuma na na tsaro. Har wa yau, babban makasudin aikin wadannan mutane shi ne samar da ingantaccen shugabanci tare da tsare rayukan mutane da dukiyoyinsu ba wani abu daban ba.

Bugu da kari, wane kokari kamfanonin sadarwa ke yi don taimakawa wajen dakile wannan matsala? Mene ne tasirin bin diddigin masu aikata laifukan? Gano kudaden haram da kuma sa ido a kan zirga-zirgar ababen more rayuwa kamar babura da wayoyin hannu, wadanda masu aikata laifuka ke amfani da su? Duk wadannan na nuna babbar gazawar tattara bayanan sirri da kuma amfani da fasaha ne.

Shin mene ne amfanin katin shedar zama dan kasa (NIN), da kuma lambar tantancewa ta banki (BBN)? Ko amfaninsu shi ne bude asusun banki ko samun lasisin tuki da fasfo na kasashen waje kadai?

 

Rashin Adalci Da Tausayi

Dangane da irin wannan ta’asa, ’yan kasa ne wadanda ba su ji ba; ba su gani ba ke daukar nauyin wannan sakaci, wadanda laifinsu kawai shi ne na zama ‘yan Nijeriya, ke fama da wahalhalu da cin zarafin da ba zai iya misaltuwa ba a hannun miyagu marasa tausayi da kuma gwamnatin da ta yi biris da hakkinsu da ke kanta.

Duk da irin wahalhalu da rashi da kuma asarar da aka yi musu, halin da suke ciki ya ta’azzara; sakamakon rashin ingantattun dokoki ko hanyoyin da za a bi don dakile ko hukunta wadannan masu laifi ko kuma samun diyya da tallafi daga gwamnati. A yayin da kukansu na neman adalci da taimako ya fada a kunnen uwar shegu tare da ci gaba da zaman dar-dar, kazalika su kuma masu aikata wannan aika-aika na nan suna yawo cikin walwala, su kuma wadanda hakkinsu ne kama masu aikata wadannan laifuka, sun shagaltu da neman karin albashi tare da yin sharholiya da kudaden gwamnati.

 

Gazawar Gwamnati Da Hukumomi

Shugabannin Nijeriya, na fuskantar wata muhimmiyar jarrabawa; wanna kuwa ita ce gazawarsu. ‘Yan majalisar dokokin kasar da aka dora wa alhakin wakilcin jama’a, sun yi biris ko kunnen uwar shegu da hakkokin jama’a da ke kansu. Yayin da hukumomin tsaron da suka hada da ma’aikatar tsaron kasar, ofishin mai ba da shawara kan harkokin tsaro da kuma rundunar ‘yan sanda; ga dukkanin alamu ba za su iya tinkarar barazanar da ke kara kamarin matsalar tsaron ba.

Har ila yau, an kwashe shekaru da dama ana gudanar da shugabanci na rashin adalci a Nijeriya, wanda wannan alama ce da za a iya gani ko a wannan gwamnati, domin kuwa bangaren zartarwa a halin yanzu na ci gaba da sayen motocin hawa, gina sabbin dakunan zama na shugaban kasa a filin jirgin sama na Abuja da gyaran gidajen gwamnati da ke Legas da Abuja, yayin da kuma sauran ‘yan Nijeriya da dama ba su da matsugunan da za su sanya duwawunsu. Wannan hali na rashin ko in kula na gwamnati, babu shakka ya bar ‘yan kasa a cikin wani mawuyacin hali.

A wannan halin da ake ciki, su kuma ýan majalisun maimakon su kafa dokoki masu tsauri don magance rashin tsaro; sai suka buge da neman a saya musu motocin alfarma kirar ‘Prado jeeps’ kowace daya a kan kudi har Naira miliyan160, motocin da ba za su iya kare su daga sharrin wadannan ‘yan ta’adda masu garkuwa da mutane ba. Yayin da su kuma jami’an tsaro suka kasa samo bakin zaren. Babu shakka, wannan babban abin takaici ne kwarai da gaske.

 

Kin Amfani Da Na’urorin Fasaha

Gwamnatoci da majalisu daban-daban da suka hada da na yanzu, sun yi ta faman farfaganda a kan batun tsaro tare da bukatar karin kudaden tsaron da kuma batun sayen jiragen ‘Tucano’ da sauran makamantansu, maimakon kalubalen tsaron da ake fuskanta ya ragu, sai ci gaba aka samu ta fuskar ta’adanci, wanda a zahiri ya nuna cewa a gaskiyar magana Nijeriya ta shafe shekaru masu yawa ta na gudanar da shugabanci maras kan-gado da adalci, wanda shi ne ya haifar da wannan yanayi na rashin tsaro da ake fama da shi a halin yanzu.

Shin zai iya yiwuwa gwamnati da sauran hukumomin tabbatar da doka da oda a ce ba su da masaniya game da sahihancin sa ido tare da samar da na’urorin bin diddigin da ka iya taimakawa wajen kawo karshen wannan ta’adanci? Ko kuwa sun yi tsada ne ko kuma Nijeriya ba ta da ma’aikatan da za su tunkari wannan aikin ne?

 

A Karshe

Tabarbarewar rashin tsaro, wata alama ce ta gazawar gwamnati da hukomomi. Don haka, ya kamata wadanda ke kan madafun iko su amince da gazawarsu tare da gyarawa ko kuma su yi murabus daga mukamansu. Yanzu lokaci ya yi da ya kamata jama’a su fara bin kadin yadda ake gudanar da mulki a kansu. Domin kuwa, jin dadin al’umma da tsaron lafiyarsu shi ne a kan gaba cikin Kudin Tsarin Mulkin Nijeriya, ba siyasa mara ma’ana irin ta wannan kasa ba.

Alhaji Adamu Rabiu ya rubuto daga Kaduna

 

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: garkuwa da mutane rashin tsaro gwamnati da

এছাড়াও পড়ুন:

Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya

Ba wannan ne karo na farko da shugaba Trump ya nuna girman kai da rashin sani game da Afirka ba. A watan da ya gabata, lokacin da yake bayani game da dalilin da ya sa gwamnatinsa ke rage gudummawar jin kai da take bayarwa a duniya, ya ce a baya, Amurka ta samar wa kasar Lesotho gudummawar dala miliyan 8, amma “ba wanda ya taba jin sunan wannan kasa”. Amma ita wannan kasar da ko sunanta shugaba Trump bai taba ji ba, ya sanya ta cikin jerin kasashen da ya sanar da zai kakaba musu haraji, har ma ya sanya mata haraji na kaso 50%. Idan ba mu manta ba kuma, a wa’adin shugabancinsa na farko, shugaba Trump ya taba bayyana kasashen Afirka a matsayin “shithole” a lokacin da ya tabo maganar bakin haure.

 

Sai dai ban da girman kai da rashin sani, kalaman shugaba Trump ya kuma bayyana matsayin da gwamnatin kasar Amurka ta dade tana dauka a game da kasashen Afirka, wato a maimakon abokan hadin gwiwa na zaman daidaito da martaba juna, tana kallonsu a matsayin abin da take iya amfani da su wajen takara da sauran manyan kasashe, kuma muna iya ganin haka ne daga manufofin da mahukuntan kasar suka dauka cikin ‘yan shekarun baya.

 

A shekarar 2014, gwamnatin Barack Obama ta shirya taron kolin Amurka da kasashen Afirka karo na farko, inda ta dauki alkawura a gaban kasashen Afirka. Sai dai bayan taron, a maimakon ta kara samar da gudummawa, sai ta rage, har da kudaden da take samarwa a fannin yaki da cutar kanjamau a Afirka. A gun taron, Amurka ta kuma yi alkawarin zurfafa huldarta da kasashen Afirka da ma gudanar da taron a kai a kai, amma ba a sake yin taron ba har sai bayan tsawon shekaru 8. A karshen shekarar 2022, Amurka ta gudanar da taron karo na biyu, inda tsohon shugaban kasar Joe Biden ya yi alkawarin samar da iya abin da kasarsa take iya bayarwa don tabbatar da kyautata makomar Afirka, kuma a cewarsa zai kai ziyara Afirka a shekarar 2023, amma bai cika wannan alkawari ba sai zuwa karshen bara, lokacin da ya kusan sauka daga kujerar shugabanci, kuma ba mu san yaushe za a cika sauran alkawuran da ya dauka ba.

 

Bayan da gwamnati mai ci ta fara aiki, jerin matakan da ta dauka sun haifar da munanan illoli ga kasashen Afirka. In mun dauki misali da harajin kwastam na ramuwar gayya da ta dauka a baya bayan nan, inda ta sanya haraji mai yawa kan kasashen Afirka 51, ciki har da 50% a kan Lesotho da 47% a kan Madagascar da 40% a kan Mauritius, matakin da ya kasance tamkar yi wa kasashen fashi. Abin lura kuma shi ne, harajin ya dakatar da dokar samar da ci gaba da damammaki a Afirka da aka san ta da AGOA, tun kafin wa’adinta ya cika, lamarin da ya jefa kasashen Afirka da dama cikin mawuyacin hali wajen yin ciniki da Amurka.

 

Har kullum kasar Sin na ganin cewa, Afirka dandali ne na hadin gwiwar kasa da kasa, a maimakon wajen yin takara tsakanin manyan kasashe. Rashin girmamawa ne ga kasashen Afirka da al’ummarsu yadda Amurka take da rashin sanin nahiyar, kuma rashin sahihancin da take wa hadin gwiwarta da kasashen Afirka ya shaida gazarwata ta daukar kasashen Afirka da muhimmanci. Kasashen Afirka na bukatar kawaye na gaske. Idan gwamnatin Trump tana son samun karbuwa daga kasashen Afirka, dole ne ta gyara matsayinta, kuma ya kamata ta fara da fahimtar kowace kasa da ke nahiyar. (Mai Zane: Mustapha Bulama)

 

 

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Talauci Da Rashin Ilimi Ne Ya Sa Ayyukan Boko Haram Ke Dawowa – Gwamnan Yobe
  • Nazarin CGTN: Ana Kara Bayyana Rashin Gamsuwa Da Sabuwar Gwamnatin Amurka Daga Ciki Da Wajen Kasar
  • Rashin tsaro: Gwamnan AbdulRahman Ya Gana Da Sarakuna Masu Daraja Ta Daya A Jihar Kwara 
  • Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Binciken Yawaitar Haɗurran Tankokin Man Fetur A Nijeriya 
  • Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
  • Gwamnatin Yobe Na Ƙoƙarin Inganta Tsaro – Hon. Idi Gubana
  • Sin Na Maraba Da Karin Abokai Daga Kasa Da Kasa Su Ziyarci Kasar
  • Akwai Ƙarin Gishiri A Yawan  Masu Sauyin Jam’iyya Zuwa APC – El-Rufai
  • Kasar Sin Za Ta Samar Da Dokar Da Ta Shafi Raya Kasa
  • Ƴan Ta’adda Sun Kashe Maharba 10 A Adamawa