Shugaba Xi Ya Yaba Da Ci Gaban Kasar Sin Duk Da Kalubalen Da Aka Fuskanta A Shekarar Dragon
Published: 27th, January 2025 GMT
A yau Litinin, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana cewa, kasar ta samu ci gaba mai inganci wajen zurfafa raya zamanantarwarta a cikin “yanayoyi masu sarkakiya da kalubale” a tsakanin watanni 12 da suka gabata.
Ya furta hakan ne yayin gudanar da wata kasaitacciyar liyafar maraba da sabuwar shekara ta kasar Sin.
Shugaba Xi wanda har ila yau shi ne babban sakataren kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin (CPC) kuma shugaban kwamitin tsakiya na sojojin kasar ya kara da cewa, “a cikin shekarar dabbar Dragon, mun nuna kuzari da ruhi mai karfi na iya aiwatarwa. Mun jure wa guguwa mai karfi kuma muka ga bakan gizo.”
Shugaba Xi a wajen liyafar, wadda kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin da majalisar gudanarwar kasar suka shirya don bikin shekarar maciji da za ta fara ranar 29 ga Janairu, ya ce, yayin da aka fuskanci yanayi mai sarkakiya da kalubale, kasar Sin ta mayar da martani cikin natsuwa tare da aiwatar da cikakkun matakai daban-daban, ta kuma yi nasarar shawo kan matsalolin, kana ta kara dagewa da kuma nuna azama. (Abdulrazaq Yahuza Jere).
এছাড়াও পড়ুন:
Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK
Kakakin ofishin jakadancin kasar Sin a kasar Birtaniya, ya soki kalaman da kasashen kungiyar G7 suka yi, dangane da ganin baiken ‘yan sandan yankin HK, bayan da a ranar 25 ga watan Yuli da ya shude, ‘yan sandan suka fitar da takardar sammacen cafke wasu mutane 19, masu yunkurin haifar da tashin-tashina a kasar Sin da suka tsere zuwa kasashen ketare.
A ranar Asabar ne ofishin jakadancin na kasar Sin a Birtaniya, ya yi tir da kalamai marasa ma’ana da kasashe membobin kungiyar G7, ciki har da Birtaniya suka furta kan batun, yana mai cewa, wasu kasashe tsiraru ciki har da Birtaniya, sun tsoma baki a batun dokar tabbatar da tsaro, wadda ‘yan sandan yankin musamman na HK ke aiwatarwa, wanda hakan katsalandan ne cikin harkokin cikin gidan kasar Sin, da ma dokokin yankin na HK. Don haka, kakakin ofishin ya ce, “Muna matukar bayyana adawa da hakan.”
Jami’in ya kara da cewa, “Muna matukar goyon bayan gwamnatin yankin musamman na HK, game da yadda take aiwatar da harkokin gwamnati bisa doka, kana muna goyon bayan ‘yan sandan yankin na HK, bisa rawar da suke takawa ta kare doka, bisa la’akari da tabbatattun dokoki.”
Ya ce, yadda hadakar wadannan kasashe suka tsoma baki cikin harkokin yankin HK, ya kara fayyace matsayarsu ta yin baki biyu, da munafurci a batutuwa masu nasaba da kare hakkin bil’adama da wanzar da doka. Kuma a cewar jami’in, ba abun da hakan zai haifar sai karfafa gwiwar gwamnatin HK, wajen jagorantar yankin bisa doka da hukunta masu laifi. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp