Belarus : Alexander Lukashenko Ya Sake Zaben Shugaban Kasa A Karo Na 7
Published: 27th, January 2025 GMT
Sakamakon farko na zaben shugaban kasa da babbar hukumar zaben kasar Belarus ta fitar da jijjifin safiyar yau Litinin ya nuna cewa, Alexander Lukashenko ne ya lashe zaben, inda ya samu kashi 86.82 cikin dari na adadin kuri’un da aka kada.
A bisa dokar kasar ta Belarus dai, ana ayyana duk dan takarar shugaban kasa da ya samu fiye da kashi 50 cikin dari na kuri’un da aka kada a matsayin wanda ya yi nasara
Hakan na nufinb Mista Lukashenko zai jagoranci kasar a wani wa’adi na mulki na bakwai na shekaru biyar.
Hukumar zaben ta sanar da fitowar kashi 81.5% na ‘yan kasar miliyan 6.9 da suka fito rumfunan zabe.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kasar Ireland Ta Sauya Sunan Shugaban “Isra’ila” Da Na Shahidiyar Falasdinu
A birnin Dublin na kasar Ireland an cire sunan tsohon sugaban “Isra’ila” Chaim Herzog,daga wata lambu na shakatawa a unguwar Ratgar, tare da maye gurbinsa da sunan Shahida Hind Rajab.
Jaridar “Vadiot-Ahranot” ta ‘yan sahayoniya ta buga labarin cewa, hukumar birnin Dublin a Ireland ta amince da a sauya sunan shugaban “Isra’ila” ta shida Chaim Herzog daga Lambun shakatawa,saboda matsin lambar kungiyoyin da suke goyon bayan Falasdinawa.
Jaridar ta ce sauya sunan wannan lambun yana da alaka ne da yakin Gaza, kuma an amince da shawarar da aka bijiro da ita a hukumar birnin ta hanyar kada kuri’u mafi rinjaye.
Wasu kungiyoyin da suke nuna goyon bayansu ga “Isra’ila” sun nuna rashin jin dadinsu da wannan matakin na sauya sunan lambun a birnin Dublin.
Lambun da aka sauya sunansa yaka kusa da wasu makarantu ne biyu na yahudawa na Firamare da sakandire da su kadai ake da su a Ireland. An bude lambun ne dai a karon farko a 1985 da sunan Oril Kowir Park’ sai dai daga baya an sa masa sunan shugaban Haramtacciyar Kasar Isra’ila na shida ” Chaim Herzog.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Sau 590 “Isra’ila” Ta Keta Tsagaiwa Wutar Yaki November 30, 2025 Washington Post: Shirin Trump Na Kai Sojojin Gaza Yana Fuskantar Matsala November 30, 2025 MDD: Kasar Somaliya Tana Fuskantar Mawuyacin Yanayi Saboda Fari November 30, 2025 An Yi Ganawa A Tsakanin Ministocin Harkokin Wajen Turkiya November 30, 2025 Iran ta bayyana halin da Falasdinawa ke ciki da rauni mufi da aka wa dan adam a doron kasa November 30, 2025 An yi gangami a fadin duniya a zagayowar ranar Falasdinu November 30, 2025 Cinikin Kasashen Waje na Iran Ya Zarce Dala Biliyan 76.5 November 30, 2025 Najeriya : Sojoji sun kubutar da yan mata 12 da mayakan ISWAP November 30, 2025 An sake zabar Eto’o a matsayin Shugaban Hukumar kwallon kafa ta Kamaru November 30, 2025 Shugaban Najeriya Ya Mika Sunaye Sabbin Jakadun Kasar su 32 Ga Majalisa Domin Tantancewa November 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci