Putin ya rattaba hannu kan yarjejeniyar hadin gwiwa da Iran
Published: 22nd, April 2025 GMT
Shugaban kasar Rasha Vladimir Putin ya rattaba hannu kan wata yarjejeniya ta hadin gwiwa daga dukkan fannoni bisa manyan tsare-tsare da Iran a hukumance, a cewar wata takardar aiki da aka wallafa a yanar gizo a jiya Litinin.
Shugaban kasar Rasha da takwaransa na Iran Masoud Pezeshkian sun rattaba hannu kan yarjejeniyar a ranar 17 ga watan Janairu bayan wata tattaunawa da bangarorin biyu suka yi a birnin Moscow.
Yayin da a ranar 8 ga watan Afrilun nan majalisar dokokin Rasha ta Duma ta amince da yarjejeniyar kana majalisar dattawan tarayyar kasar suka amince da yarjejeniyar a ranar 16 ga Afrilu.
Bisa yarjejeniyar da aka cimma, kasashen biyu na da burin zurfafa da fadada dangantakarsu a dukkan fannonin da suka shafi moriyar juna, da karfafa hadin gwiwa a fannin tsaro, da hada kai wajen gudanar da harkoki a matakin shiyya-shiyya da na duniya baki daya, wanda ya dace da cikakken kawance bisa manyan tsare-tsare kuma na dogon lokaci.
Kazalika, Putin ya jaddada muhimmancin yarjejeniyar, yana mai cewa, ta zayyana “manufar da aka sanya gaba” na zurfafa hadin gwiwa na dogon lokaci.
Kuma an tsara yarjejeniyar ne domin samar da kwanciyar hankali ga dorewar ci gaban kasashen biyu da ma daukacin yankin Eurasia.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: hadin gwiwa
এছাড়াও পড়ুন:
Sabbin Bayanai Kan Fashe-Fashe Wasu Abubuwa A Tashar Jiragen Ruwan Kasar Iran
Gwamnan lardin Hormozgan (mai hedikwata a Bandar Abbas), Mohammad Ashouri, ya ce wani bangare na lamarin tashar jiragen ruwa na Shahid Raja’i ya faru ne sakamakon keta sanarwar adana kayayyaki ne, wani bangaren kuma na da alaka da sakaci da rashin kulawa (a wajen ajiya).
AShouri, wanda ya bayyana ta hanyar faifan bidiyo a wata hira da aka watsa ta talabijin a yammacin jiya Litinin, ya bayyana sabbin alkaluman wadanda suka bata: Akwai mutanekusan 22 da suka bace, kamar yadda wasu gawarwakin mutane 22 ba a iya tantace su ba ko su waye ba.
Ya ce: “Wasu daga cikin wadanda suka jikkata an hanzarta jigilar su ta jirgin saman soja zuwa asibitin birnin Shiraz.”
Gwamnan lardin Hormozgan na Iran ya ce: An cimma wasu bincike na farko dangane da yiyuwar yin sakaci a wannan fanni, kuma ana gudanar da bincike sosai kan dukkan al’amuran da suka faru. Kuma babu wata daga kafa da za a yi ga duk wanda aka samu da yin sakaci a kan haka za a tuhume shi kamar yadda shari’a ta tanada.
Ya ci gaba da cewa, “Ta hanyar nazarin faifan bidiyo daban-daban na aukuwar lamarin tashar jirgin ruwa ta Shahid Raja’i, an lura da cewa, an yi jigilar kaya a lokacin da lamarin ya faru, inda hayaki ke tashi, sai kuma fashewar wani abu.