HausaTv:
2025-07-31@10:02:38 GMT

Putin ya rattaba hannu kan yarjejeniyar hadin gwiwa da Iran

Published: 22nd, April 2025 GMT

Shugaban kasar Rasha Vladimir Putin ya rattaba hannu kan wata yarjejeniya ta hadin gwiwa daga dukkan fannoni bisa manyan tsare-tsare da Iran a hukumance, a cewar wata takardar aiki da aka wallafa a yanar gizo a jiya Litinin.

Shugaban kasar Rasha da takwaransa na Iran Masoud Pezeshkian sun rattaba hannu kan yarjejeniyar a ranar 17 ga watan Janairu bayan wata tattaunawa da bangarorin biyu suka yi a birnin Moscow.

 

Yayin da a ranar 8 ga watan Afrilun nan majalisar dokokin Rasha ta Duma ta amince da yarjejeniyar kana majalisar dattawan tarayyar kasar suka amince da yarjejeniyar a ranar 16 ga Afrilu.

Bisa yarjejeniyar da aka cimma, kasashen biyu na da burin zurfafa da fadada dangantakarsu a dukkan fannonin da suka shafi moriyar juna, da karfafa hadin gwiwa a fannin tsaro, da hada kai wajen gudanar da harkoki a matakin shiyya-shiyya da na duniya baki daya, wanda ya dace da cikakken kawance bisa manyan tsare-tsare kuma na dogon lokaci.

Kazalika, Putin ya jaddada muhimmancin yarjejeniyar, yana mai cewa, ta zayyana “manufar da aka sanya gaba” na zurfafa hadin gwiwa na dogon lokaci.

Kuma an tsara yarjejeniyar ne domin samar da kwanciyar hankali ga dorewar ci gaban kasashen biyu da ma daukacin yankin Eurasia.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: hadin gwiwa

এছাড়াও পড়ুন:

Nijar da Rasha sun ƙulla yarjejeniyar makamashin nukiliya

Jamhuriyar Nijar da ƙasar Rasha a ranar Litinin, 28 ga watan Yulin 2025 sun ƙulla yarjejeniya game da makamashin nukiliya da kuma haƙar yuraniyom.

Kamfanin dillancin labaran Nijar (ANP) ya ruwaito cewa ƙasashen biyu sun rattaba hannu a kan yarjejeniyar ce bayan ganawar shugaban Nijar, Janar Abdourahamane Tiani, da wata babbar tawagar Rasha ƙarƙashin jagorancin Ministan Makamashi, Mista Sergei Tsivilev.

Ambaliya ta yi ajalin mutum 30 a China Jami’ar Jihar Gombe za ta fara sabbin darussa 6 a fannin noma

“Muhimmiyar manufarmu ita ce mu ƙara inganta rayuwar mutanen Nijar da na Rasha,” in ji Sergei, kana ya bayyana cewa sun rattaba hannu kan wata yarjejeniya game da makamashin nukiliya da haƙar yuraniyom.

“Mun amince cewa za mu horar da manyan jami’ai waɗanda za su iya aiki a fannonin tallafinmu irin na makamashi da noma da lafiya da ilimi, kuma za mu horar da injiniyoyi tun a makarantu domin su ci gaba da karatunsu a jami’o’in da ke Tarayyar Rasha,” in ji shi.

Ganawar ta mayar da hankali ne kan dangantaka tsakanin Tarayyar Rasha da Nijar, in ji rahoton na ANP.

Bayan ganawar dai Ministan na Rasha ya bayyana godiyarsa ga shugaba da mutanen Nijar domin irin tarbar da aka yi masa.

“Mun ga bayanai da dama game da damarmakin da ke akwai a cikin Nijar, kuma a halin yanzu mutanenmu na ƙoƙarin aiki kan damarmakin da ke nan a Nijar,” in ji Mista Sergei Tsivilev, wanda shi ne shugaban ɓangaren Rasha a hukumar haɗakar gwamnatoci da ƙasashen AES.

“Shugaban ƙasar ya kuma sanar da mu cewa shi zai zaɓi shugaba na ɓangare ɗaya na hukumar haɗakar gwamnatocin nan ba da jimawa ba domin ayyukanmu da ‘yan uwanmu na Nijar su yi ta tafiya babu tangarɗa,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana
  • Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da Amurka
  • Amincewa Da Kasar Falasɗinu: Birtaniya Ta Gindaya Wa Isra’ila Sharuɗɗa
  • Kasashen Iran Da Rasha Sun Tattauna Batun Hadin Gwiwar Kafofin Watsa Labarai A Tsakaninsu
  • Nijar da Rasha sun ƙulla yarjejeniyar makamashin nukiliya
  •  Kasar Holland Ta Hana MInistocin HKI Biyu Shiga Cikin Kasarta
  • Kasar Iran Ta Musanta Yin Katsalandan A Tattaunawar Neman Tsagaita Bude Wuta A Gaza
  • Kasar Faransa Ta Yi Allah Wadai Da Harin Ta’addancin Da Aka Kai Birnin Zahedan Na Kasar Iran
  • Wakilin Gidan Talabijin Na Al-Alam Ya Bayyana Yadda Shi Da Iyalansa Suka Rayu Kwanaki Biyu Babu Abinci A Gaza
  • Iran Ta Ce Amurka Ce Bayan Hare-haren Da Aka Kai Zahidan