Aminiya:
2025-09-17@21:49:05 GMT

Jiragen yaki sun kashe ’yan ta’adda 35 a iyakar Najeriya da Kamaru

Published: 25th, August 2025 GMT

Sojojin Najeriya sun kashe ’yan ta’adda kimanin 35 da ake zargin mayakan kungiyar ISWAP ne a kusa da iyakar Najeriya da Kamaru.

’Yan ta’addan sun taru a yankin Kumshe, wani gari da ke kan iyaka a Jihar Borno, da safiyar Asabar domin kai hari kan sansanin sojoji da ke yankin.

Majiyoyin tsaro sun bayyana cewa bayan samun bayanan sirri, sojojin kasa sun nemi taimakon rundunar sojin sama, inda jiragen yaki suka kai hare-hare a wuraren da aka gano ’yan ta’addan sun taru.

“Ranar Asabar, 23 ga Agusta, sojojin runduna ta 21 sun dakile wani hari da ’yan ta’adda suka kai da daddare, inda jiragen yaki suka ragargaza ’yan ta’addan,” in ji wata majiya.

Binciken bayan harin ya nuna cewa an binne gawarwaki fiye da 20, ciki har da sassan jikin da suka tarwatse, an kuma kwato makamai daga hannun ’yan ta’addan.

Kakakin rundunar sojin sama, Iya Komodo Ehimen Ejodame, ya tabbatar da harin, yana mai cewa fiye da ’yan ta’adda 35 ne aka kashe a hare-haren.

Ya ce rundunar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen murkushe ’yan ta’adda a Arewa maso Gabas da Arewa maso Yamma.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hare hare jiragen yaki yan ta addan yan ta adda

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Ambaliyar ruwa na cigaba da salwantar da dukiyoyi da rayukan al’ummomi da dama a sassa daban-daban na Najeriya.

 

Ko a farkon makon nan, hukumomi sun yi gargadin cewa akwai yiwuwar samun ambaliyar a jihohi akalla 11.

Sai dai wasu alummomin tuni suka dauki matakai don rage barnar da ambaliyar ka iya yi musu.

NAJERIYA A YAU: Masu Nau’in Jinin AS Sun Fi Masu Nau’in AA Lafiya DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa Nayi Yunkurin Kashe Kaina Har Sau Uku

A kan wadannan matakai shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Microsoft ya ƙwace shafukan wasu kamfanoni 340 a Najeriya
  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba
  • Akalla Falsdinawa 78 Ne Suka Yi Shahada A Yau A Gaza.
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
  • Sarki Sanusi II ya koka kan yawan cin bashin Najeriya
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa