Aminiya:
2025-11-02@20:55:57 GMT

Wata mata ta mayar da N4.8m da aka yi kuskuren tura wa asusunta a Maiduguri

Published: 25th, August 2025 GMT

Wata mata mai aikin shara da goge-goge, Fa’iza Abdulkadir, ta mayar da kuɗi har N4.8m da aka yi kuskuren tura wa asusun bankinta a Maiduguri, babban birnin Jihar Borno.

Da take zantawa da News Central a Maiduguri, Fa’iza wadda take ɗaukan albashin Naira dubu 30 duk wata ta ce ta yanke shawarar mayar da kuɗin ne saboda tsoron Allah.

An yaudari ’yan Nijeriya da suka hana Jonathan lashe Zaɓen 2015 — Ƙungiya Za a yi amfani da Hausa wajen samar da zaman lafiya — Abdulbaqi Jari

“Wannan kuɗi ba haƙƙi na ba ne, ba ni na mallaki kuɗin ba, shi ya sa na mayar. Na fi son na zauna cikin kwanciyar hankali da kuma gudun azabar Allah a ranar lahira,” in ji ta.

Fa’iza ta bayyana cewa ta shafe kwanaki uku tana zaraya a banki kafin ta kammala duk matakan mayar da kuɗin.

“Na shafe kwanaki uku babu sukuni don ko abincin kirki ba na samu na ci yadda kamata har sai da na mayar da kuɗin, sannan na samu kwanciyar hankali,” in ji ta.

Ma’aikatan banki da maƙwabta a unguwar da take zaune sun bayyana Fa’iza a matsayin mace mai gaskiya wadda take rayuwa da albashin N30,000 da take samu daga wata cibiyar lafiya inda take aiki.

“Ba abin mamaki ba ne, saboda yadda take da tarbiyya da kuma yadda take renon ‘ya’yanta.

“Tana da kyawawan ɗabi’u, kuma tana rayuwa cikin rufin asiri da ‘ya’yanta guda biyar,” in ji wata maƙwabciyarta.

Wani jami’in banki ya ce abin da Fa’iza ta yi ya ba mutane mamaki sosai. “Duk da halin da take ciki, ta ji tsoron Allah ta yi abin da ya dace.

“Na taɓa ganin irin haka ta faru a wannan banki inda aka yi kuskuren tura kuɗi a asusun wani, ya cire kuɗin ya kashe.

“Sai da ya jefa ma’aikatan banki cikin tashin hankali don hatta ‘yan sanda sun shiga lamarin, amma har yanzu ba a dawo da kuɗin ba,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: jihar Borno

এছাড়াও পড়ুন:

Barcelona ta shiga zarwacin Victor Osimhen

Kungiyar ƙwallon ƙafa ta Barcelona da ke Sipaniya na ƙoƙarin ɗauko Victor Osimhen a matsayin wanda zai maye gurbin Robert Lewandowski wanda ke fama da matsalar raunuka

Ɗan jaridar ƙasar Sifaniya, Gabriel Sans na Mundo Deportivo ya bayyana cewar, Barcelona na neman wanda zai maye gurbin Robert Lewandowski a matsayin mai jefa ƙwallo a raga, hakan ne ya sa ƙungiyyar ta amince da ɗaukar Osimhen.

’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA

A ƙarshen kakar bana ne ake tunanin up Lewandowski zai bar Barca, wanda zai tilasta wa ƙungiyyar neman wani zaƙaƙurin ɗan wasan gaba mai ciyo ƙwallo.

Victor Osimhen dai a bazarar nan ne ya koma Galatasaray bayan barin Napoli ta Italiya.

Osimhen dai ba ya ɓoye aniyarsa ta buga wasa a ɗaya daga cikin manyan gasannin Nahiyyar Turai biyar ba, ciki har da Firimiya ta Ingila da LaLiga ta Sifaniya, inda Barcelona ke cikin manyan ƙungiyoyin gasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Allah Ya yi wa Malam Nata’ala rasuwa
  • IAEA : Babu wata shaida da ke nuna cewa Iran na kera makaman nukiliya
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini
  • Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa
  • Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace
  • Barcelona ta shiga zarwacin Victor Osimhen
  • ’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi
  • Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar
  • Yan Nijeriya Na Ɗanɗana Kuɗarsu Kan Jinkirta Cire Tallafin Mai – Sarki Sanusi
  • Allah Ya Kai Manzon Allah (SAW) Muƙami Na Babban Yabo A Cikin Komai