Aminiya:
2025-09-17@21:51:39 GMT

Rushe Kasuwar Alaba Rabo: ’Yan Arewa sun bukaci a biya su diyya

Published: 25th, August 2025 GMT

’Yan Arewa a Kasuwar Alaba Rago, shahararriyar kasuwar ’yan Arewa a Jihar Legas sun roki gwamnatin jihar ta biya su diyya kan asarar da suka yi sakamakon rushe kasuwar da gwamnati nta yi.

Sun bayyana cewa asarar da suka tafka ta haura Naira biliyan 20 bayan Gwamnatin Legas ta rusa masallatai sama da 40 da shaguna kimanin 3,000 a Kasuwar wadda suka kafa shekara 45 da suka gabata a jihar.

A karo na biyu a ’yan kwanakin nan mahukunta a Jihar Legas suka rushe sassa da dama na kasuwar, wadda ta yi fice da kasuwancin kayan abinci da dabbobi da karafa da sauran kayan masarufi, wacce Hausawa suka kafa a shekarar 1979.

A cikin watan Mayun 2024, jami’an hukumar ’yan sandan jihar Legas sun mamaye kasuwar, inda suka ce an gudanar da aikin ne domin kawar da bara-gurbi a kasuwar.

NAJERIYA A YAU: Kalubalen Da Iyaye Ke Fuskanta Wajen Tarbiyyan ‘Ya’yan Su Yau Shugabannin Tsaron Afrika 54 ke taro a Abuja Zargin N6.5bn ya dabaibaye hadimin Gwamnan Kano

A ranar Lahadin makon jiya, 17 ga watan Agusta, kuma aka fara rusau na baya-bayan nan a kasuwar, lamarin da ya ci gaba zuwa ranar Laraba 20 ga watan Agustan, inda dubban ’yan kasuwa suka rasa matsugunnansu.

Alhaji Adamu Katagum, Wazirin Sarkin Alaba Rago, ya shaida wa Aminiya cewa sama da shaguna 3,000 ne aka rushe ciki har da masallatai 40, inda ya kiyasta cewa asarar da ’yan kasuwa suka yi ya haura Naira biliyan 20.

Ya ce ’yan Arewa ne suka kafa kasuwar tun lokacin da wajen yake jeji ne da kuzazzabai, inda suka zuba jari mai yawa don bunkasa ta.

“A wancan lokacin, wannan wurin ya kasance da kurmi da fadama, babu hanyar sadarwa, ‘yan kasuwa Hausawa ne suka bunkasa ta da albarkatunsu da kuma kudin shigarsu tsawon shekaru da dama.

“Gwamnati ba ta taba kashe ko sisi daya a nan ba, duk da haka muna biyan haraji da hakkin gwamnati a kowane mataki, sai suka zo suka rushe abin da muka yi ta yi tsawon shekaru 50 muna ginawa ba tare da bin ka’ida ba, wannan babbar asara ce ga mu ’yan Arewa da ke kokarin samun abin dogaro da kai a nan,” Inji Katagum.

Ya kuma bayyana takaicinsa, inda ya ce, “Mun shafe sama da shekara 50 muna gina wannan kasuwa, mun sha wahala wajen kafa sana’o’inmu a nan, kuma a rana guda suka rusa komai ba tare da gargadi ba, mun kirga akalla masallatai 40 da aka lalata.”

Wani da abin ya shafa, Alhaji Muhammed Rabiu ’Yan Masarain, ya koka da abin da ya bayyana a matsayin rashin adalci duk da irin gudunmawar da ’yan kasuwar ke bayarwa wajen bunkasa tattalin arzikin Jihar Legas.

Ya kara da cewa al’ummar yankin sun goyi bayan jam’iyya mai mulki a Legas tun a shekarar 1999, kuma ya ce wannan ba hanya ce da ta dace ba don saka musu da biyayyar da suke yi.

“Mu ’yan Najeriya ne, kuma Legas wani bangare ne na Najeriya, muna da ’yancin kasancewa a nan, inda muka zauna muna fatauci tunda ba komai ba ne sai fadama. Mu ba zaune muke a matsugunan da ba bisa ka’ida ba ne, kadarorinmu suna da takardun doka, kuma muna biyan duk haraji da ake bukata.

“Duk da haka, mun tashi ne a safiyar ranar Litinin, sai muka yi taho-mu-gama da ’yan sanda dauke da makamai, wadanda suka yi rakiya ga wadanda suka rusa mana dukiyoyinmu da rayuwarmu suka ruguje su cikin kiftawa da bisimillah,” inji Rabiu a cikin wata murya mai cike da damuwa.

Kawo yanzu dai ’yan kasuwar na ci gaba da kasuwanci a yashe cikin rana da dari yayin da ruwan sama ke bugun su a lokacin da ya sauka.

Zuwa lokacin hada wannanl labairn yanzu Gwamnatin Jihar Legas ba ta fitar da wata sanarwa ba game da aikin na rusau da aka yi a daya daga cikin kasuwannin jihar da ke tara jama’ar Arewa, kuma kasuwa mafi yawan jama’ar Arewa jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan kasuwa Alaba Rago Arewa Gawmnatin Jihar Legas Kasuwar Alaba Rago Yan Arewa Jihar Legas jihar Legas

এছাড়াও পড়ুন:

Hamas ta bukaci kasashen musulmi da na Larabawa su dauki mataki mai tsari kan Isra’ila

Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta yi kakkausar suka ga harin da Isra’ila ta kai kan Qatar a baya-bayan nan, inda ta bukaci kasashen Larabawa da na musulmi da su dauki matsaya daya kan matakan wuce gona da iri na gwamnatin mamayar.

Basem Naim, mamba a ofishin siyasa na kungiyar Hamas,ne  ya yi wannan kiran a cikin wata sanarwa a ranar Lahadi, yayin da ministocin harkokin wajen kasashen Larabawa da na kasashen musulmi suka halarci taron gaggawa na Doha, domin tattauna harin da Isra’ila ta kai kan shugabannin Hamas a kasar Qatar.

Babban jami’in na Hamas ya yi kira ga shugabannin yankin da ke halartar taron da su mayar da Isra’ila saniyar ware a siyasance da ta fuskar tattalin arziki da kuma gurfanar da jami’an Isra’ila a kotunan duniya domin kawo karshen yakin kisan kare dangi a Gaza.

Naim ya kuma jaddada cewa, harin da Isra’ila ta kai kan tawagar Hamas a birnin Doha, ya zo ne a daidai lokacin da tawagar ke tantance wata sabuwar shawarar tsagaita bude wuta a Gaza.

“Mun nuna sassauci mafi girma na kawo karshen kisan kiyashin da ake yi a Gaza, amma sojojin mamaya ne, ta hanyar amfani da kisa da kuma sanya sharuddan nasu, ke kawo cikas ga duk wata yarjejeniya da za a iya cimma.”

Daga karshe ya bayyana cewa kungiyar Hamas tana sa ran taron zai dauki matsaya guda daya mai ma’ana tsakanin Larabawa da musulmi, da suka hada da tsagaita bude wuta nan take da kawo karshen yakin Gaza, da dage shingen da aka yi, da yanke duk wata alaka da Isra’ila, da gurfanar da isra’ila kan laifuffukan da ta aikata, da samar da falasdinu mai  ‘yancin cin gashin kai, da Al-Quds a matsayin babban birninta, da kuma tabbatar da ‘yancin komawar ‘yan gudun hijira.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Rabin Sojojin Isra’ila da suka ji rauni a yakin Gaza na fama da ciwon damuwa September 15, 2025 Sudan ta soki takunkuman da Amurka ta kakaba mata September 15, 2025 Dakarun Sojin Yamen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Ramon Na Isra’ila. September 14, 2025 Isra’ila Za ta Gamu Da Mummunar Martani Idan Tayi Gigin Afkawa Iran September 14, 2025 Ministocin Harkokin Wajen Kasashen Larabawa Da Na Musulmi Sun Fara Taro A Qatar. September 14, 2025 Gwamnatin Najeriya Ta Sanar Da Sabon Sharadi Na Bude Asusun Banki September 14, 2025 An Zabi Issa Tchiroma A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A Kamaru September 14, 2025 Kasar Iran Ta Yi Fatali Da Zarge-Zargen Da Kungiyar G7 Da Kawayenta Suka Yi Kanta September 14, 2025 Iran Ta Bayyana Shirinta Na Halartar Taron Shekara-Shekara Na Hukumar Makamashin Nukiliya September 14, 2025 Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Bayyana Rashin Halarta Tawagarta A Kada Kuri’a Kan Batun Falasdinu   September 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 
  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
  • NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago
  • Hamas ta bukaci kasashen musulmi da na Larabawa su dauki mataki mai tsari kan Isra’ila