Za a yi amfani da Hausa wajen samar da zaman lafiya — Abdulbaqi Jari
Published: 25th, August 2025 GMT
Za a yi amfani da harshen Hausa a matsayin hanyar samar da zaman lafiya a yayin bikin Ranar Hausa ta Duniya karo na goma (10), wanda za a gudanar a Daura da ke Jihar Katsina, a ranar Talata, 26 ga watan Agusta, 2025.
Jagoran taron, Abdulbaqi Aliyu Jari, wanda shi ne ya ƙirƙiri wannan rana, ya bayyana hakan yayin da yake zantawa da manema labarai a Katsina.
Ya ce dukkan shirye-shirye sun kammala, kuma manyan baƙi daga ciki da wajen Najeriya tuni sun fara isowa domin halartar bikin.
Jari ya ce an tsara taron ne domin baje kolin al’adun Hausawa da kuma jaddada muhimmancin harshen Hausa a matsayin alamar alfahari da haɗin kai.
A cewarsa, za a yi baje kolin kayan tarihi da dama, ciki har da hawan doki, sana’o’in gargajiya, saƙa da sauran su, domin nuna gadon al’adu da darajar harshen Hausa.
Ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta jihohi da su ƙara bai wa harsunan asali dama, musamman Hausa wanda mutum fiye da miliyan 200 ke amfani da shi a duniya.
Ya ƙara da cewa lokaci ya yi da Hausa za ta samu ƙarin ƙarfafawa a matsayin harshen ƙasa a hukumance, duba da yaɗuwar harshen musamman yadda ya ƙetare iyakokin Najeriya zuwa wasu ƙasashen Afirka ta Yamma, ƙasashen ECOWAS da maƙwabta.
“Idan aka amince da Hausa a matsayin harshen ƙasa, hakan zai ƙara sauƙaƙa mu’amala, ya bunƙasa kasuwanci, ya inganta alaƙa tsakanin jama’a, tare da taimakawa wajen samar da zaman lafiya,” in ji shi.
Taken bikin na bana shi ne: “Amfani da Harshen Hausa Don Samar da Zaman Lafiya.”
Abdulbaqi ya bayyana cewa manufar babban taron shi ne ƙarfafa fahimtar juna da wayar da kan jama’a kan rawar da harshen Hausa da al’adun Hausawa za su iya takawa wajen wanzar da zaman lafiya.
Kazalika, Jari ya ce ana sa ran halartar gwamnoni, ministoci, sarakunan gargajiya da manyan baƙi daga sassa daban-daban na ƙasar, tare da kira ga jama’a daga nesa da kusa da su hallara a Daura domin shaida baje kolin al’adun Hausawa a idon duniya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Abdulbaqi Aliyu Jari Bikin Ranar Hausa Daura Jihar Katsina Ranar Hausa ta Duniya da zaman lafiya harshen Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Sanya Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3
Gwamnatin kasar Iran ta sanar da ranar 30 ga watan nuwambar kowacce shekara a matsayin ranar kasa ta tsibirin Abu Musa tumbu babba da tumbu karami da ta karbo daga hannu birtaniya a shekaru da suka gabata, wanda yayi daidai da 9 ga watan Azar na kalandar iraniyawa .
Tsibiran guda 3 da ake takaddama akansu Abu musa da tunbu babba da karami suna yankin tekun fasha ne tsakanin mailand na iran da kuma hadaddiyar daular larabawa, tsibbiran wani bangare ne na kasar iran tun karnoni da suka gabata da ke cike da abubuwa da suka safi doka da tarihi a iran da kuma kasa da kasa.
Iran ta jaddada cewa dukkan wadannan tsibirai guda 3 wani bangare na kasarta da babu tantama akai,don haka ta yi kira ga kasashen larabawa da su guji daukar duk wani mataki akai da zai iya cutar da dangantakar dake tsakaninsu.
A ranar 30 ga watan nuwambar shekara ta 1971 ne dakarun birtaniya suka janye daga tsibiran kuma kwana biyu kafin kafa hadaddiyar daular larabawa a hukumance aka dawo da ikon mallakar tsibiran ga kasar iran bisa doka.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka HKI Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza Inda Take Kashe Falasdinawa October 31, 2025 An Tube Yarima Mai Jiran Gado Na Birtaniya Bayan Da Aka Tabbatar Da Laifinsa October 31, 2025 Kasashen Pakistan Da Afghanistan Sun Tsawaita Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta October 31, 2025 M D Duniya Tayi Gargadi Game Da Gwajin Nukiliya Da Amurka Ta Sanar Za ta yi October 31, 2025 Sudan Ta Yi Kira Ga Kwamitin Tsaro Da Ya Ayyana RSF A Matsayin Kungiyar ‘Yan Ta’adda October 31, 2025 Araqchi: Gwajin Makaman Nukiliya Na Amurka Babbar Barazana Ce Ga Duniya October 31, 2025 Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan October 31, 2025 Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Kutsen Na Isra’ila A Kudancin Kasar October 31, 2025 Madagascar Ta Sanar da Kafa Sabuwar Gwamnati Tare da Manyan ‘Yan Adawa October 31, 2025 Iran ta yi fatali da kalamman IAEA Kan Shirin Nukiliyarta October 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci