Dangantaka ta yi tsami tsakanin Aljeriya da kasashen kawancen Sahel
Published: 8th, April 2025 GMT
A wani mataki na mayar da martani da nuna fishi, kasar Aljeriya ta yi wa jakadunta a kasashen Mali, da Nijar kiranye, tare da jinkirta aikewa da jakadanta a Burkina faso, bayan da kasashen guda uku na kawacen sahel suka dau irin wannan matakin domin goyan bayan Mali, bisa takadamar dake tsakaninta da Aljeriya biyo bayan kakkabo jirginta marar matuki.
Haka zalika ma’aikatar tsaron kasar Aljeriya ta sanar da rufe sararin samaniyarta ga dukkan jiragen da ke zuwa kasar Mali”, ba tare da bayar da wani karin bayani ba, wanda ke nuni da cewa jiragen farar hula na kasuwanci da kamfanonin jiragen sama na kasa da kasa su ma abin ya shafe su.
Takaddama dai ta yi zafi tsakanin Aljeriya da Mali, inda ita ma Bamako ta sanar a yammacin ranar Litinin cewa, za ta rufe sararin samaniyarta “ga dukkan jiragen saman farar hula da na soji da ke tashi ko isa Algeria.”
Amma, rufe sararin samaniyar Aljeriya bai shafi kawayen Mali wato Nijar da Burkina Faso ba, saidai Aljeriyar ta ce ba yi nadama kan yadda kasashen suka biyu suka dau irin wannan matakin ba na goyan bayan Mali ba tare da tunani ba.
A ranar Lahadi ne Kasashe uku na AES suka sanar da yin kira ga jakadun su da ke kasar Aljeriya.
A cikin wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen kasar Aljeriya ta fitar, ta yi watsi da “mummunan zarge-zargen” da kasar Mali ta yi, inda ta ce Algiers ta harbo daya daga cikin jiragenta marasa matuka a kan kasarta.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Aljeriya
এছাড়াও পড়ুন:
Jagora Ya Bada Umurnin A Gudanar Bincike Mai Zurfi A Fashewar Tashar Jiragen Ruwa Na Shaheed Rajae
Jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khaminae, a karon farko da yayi magana dangane da fashewar tashar jiragen ruwa na Shahida Rajae ya gabatar da Ta’ziyya ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu ko suka jikata a wannan hatsarin. Ya kuma bukaci a gudanar da bincike mai mai zurfi don gano musabbabin fashewar.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto jagoran yana bada umurni ga ma’aikatar shari’aa a kasar ta gudanar da cikekken bincike don sanin abinda ya faru saboda daukar matakan da suka dace don hana irin wannan sake faruwa nan gaba, sannan idan akwai wadanda suka yi kuskure a hukunta su.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa gobarar da ta taso a tashar jiragen ruwa na Shahid Rajae, daya daga cikin tashoshin jirage masu muhimmanci a tattalin arzikin kasar, don haka dole ne a kara daukar matakan tsaro da amincin tashar don hana irin wannan sake faruwa.
Sanadiyyar wannan hatsarin majalisar dokokin kasar ta shelanta makoki a duk fadin kasar a yau Litinin. Sannan shugaban kasa Masoud Pezeshkiyan ya ziyarci tashar jiragen ruwa na Shahida Rajae don ganewa idanunsa abubuwan da suka faru da kuma barnan da aka tabka.
Ya zuwa yanzun wadanda suka rasa rayukansu sun kai 40 sannan wadanda suka rasa rayukansu sun kai dubu guda.