Gwamnatin Jigawa Za Ta Rika Bayar Da Maganin Hawan Jini Da Siga Kyauta
Published: 7th, April 2025 GMT
Gwamnatin jihar Jigawa ta ce za ta bullo da shirin bada magani kyauta ga masu cutar siga da hawan jini da kuma sikila.
Kwamishinan lafiya na jihar, Dr Abdullahi Muhammad Kainuwa ya bayyana haka ga manema labarai a Dutse.
Yace tuni gwamna Umar Namadi ya bada umarnin gabatar masa da wannan kudiri domin aiwatar da shirin don kula da lafiyar al’ummar jihar musamman masu karamin karfi.
Dr Abdullahi Kainuwa yana mai cewar a yanzu haka gwamnatin jihar tana gudanar da aikin Dandamalin sabon asibitin kashi na garin Gumel kan naira miliyan 380.
A cewar sa, za a bada kwangilar sayen kayayyakin asibitin Kashi na naira miliyan dari shida.
Kwamishinan ya kara da cewar gwamnatin jihar ta kammala aikin gina dakunan wankin Koda a manyan asibitocin Dutse da Ringim da kuma Kazaure.
Yana mai cewar za a bada kwangilar sayo kayayyakin aikin dakunan domin fara wankin koda kyauta ga al’umma kafin karshen shekarar nan da muke ciki.
Dr Kainuwa, yace a yanzu haka ana wankin koda kyauta a asibitocin garuruwan Gumel da kuma Hadejia.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Kungiyar Hizbullah Ya Abbaci Abubuwa 3 Wadanda Yakamata Kasar Ta Maida Hankali A Kansu
Shugaban kungiyar hizbullah ta kasar Lebanon Sheikh Na’imKasim ya bayyana cewa, kungiyarsa tare da Sojojin kasar da kuma mutanen kasar ne zasu tabbatar da ci gaban kasar Lebanon a wannan halin da ake ciki.
Tashar talabijin ta Al-Mayadeen ta nakalto sheikh Na’im kasim yana fadar haka a wani jawabin da ya gabatar a jiya Litinin, jawabinda kafafen yada labarai da damaa suka watsa kai tsaye.
Sheikh Qasim kasar Lebanon zata ci gaba da zama mai karfi idan gwamnatin kasar ta dakatar da hare-haren da HKI take ci gaba da kawowa a kan kasar, da kwato dukkan yankunan kasar da aka mamaye, har’ila yau da kuma ci gaba da hadin kai tsakanin masu gwagwarmaya, sojoji da kuma mutanen kasar.
Shugaban kungiyar ya jadda bukatar sake gina wuraren da HKI ta rusa a yankunan daban daban a kasar, ya ce gwamnatin kasar ta yi alkawalin zata sake gina wuraren da HKI ta rusa a yakin da hizbullah a baya-bayan nan.
Kuma ya ce rashin yin haka nuna bambanci ne a tsakanin mutanen kasar. Ya ce dangane da wadanda aka rusa gidajensu kungiyar ta bada kudaden haya ga 50,755 , sannan ta gyura wasu 332 da aka lalata, wanda duk aikin gwamnati ne ta yi hakan. Don haka akwai bukatar gwamnati ta aikata wajibin da ya hau kanta.