Gwamna Umar Namadi Ya Taya Al’ummar Musulmi Murnar Bikin Sallah Karama
Published: 31st, March 2025 GMT
Gwamna Umar Namadi na Jihar Jigawa ya taya al’ummar Musulmi murna bisa kammala azumin watan Ramadan lafiya, tare da kira garesu da su rungumi koyarwar Annabi Muhammadu (S.A.W) a cikin rayuwarsu ta yau da kullum.
Ya bayyana hakan ne a sakon sa na Sallah ga al’ummar jihar.
Malam Umar Namadi ya yi addu’a ga Allah Madaukakin Sarki da ya karɓi azumi da addu’o’in al’ummar Musulmi da suka yi a watan na Ramadan.
Haka kuma, ya roƙi Allah Madaukakin Sarki da ya ci gaba da yi wa shugabanni jagorancin don yin abin da ya dace domin jin daɗin al’umma.
Namadi ya kuma yi addu’ar samun zaman lafiya, da hadin kai, da ci gaban tattalin arzikin ƙasa.
Radiyon Najeriya ya ruwaito cewa, Gwamnan ya kuma karɓi manyan baki da suka kai masa gaisuwar Sallah a Fadar Gwamnati da ke Dutse.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Jihar Jigawa Ce Ta Fara Biyan Kudaden Kujerun Aikin Hajjin 2026- NAHCON
Hukumar Aikin Hajji ta Kasa NAHCON ta yi kira ga jihohin kasar nan da su yi koyi da Gwamna Umar Namadi na Jihar Jigawa wajen tare kujerun aikin hajji domin baiwa Maniyatan su damar sauke farali.
Kwamishina a hukumar mai kula da shiyyar arewa maso yamma , Sheikh Muhammad Bin Usman yayi wannan kiran a lokacin da ya kai ziyarar aiki a Dutse, babban birnin Jihar.
Sheikh Muhammad Bin Usman yayi bayanin cewar, ya zama wajibi ga sauran hukumomin Alhazan kasar nan da su yi koyi da Gwamna Umar Namadi wajen bai wa hukumomin Alhazai bashin kudade domin tare kujerun aikin Hajji ga maniyata.
Yana mai nuni da cewar, a halin yanzu, jihar Jigawa ce ta farko wajen biyan kujerun aikin Hajjin 2026 a fadin kasar nan.
Babban malamin ya kuma yabawa Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa Alhaji Ahmed Umar Labbo bisa namijin kokarin sa wajen shirye shiryen aikin Hajji akan lokaci.
Da ya waiwayi batun hadaya kuma, Sheikh Bin Usman yace a duk fadin kasar nan, jihar Jigawa ce take da lasisin yin Hadaya ga maniyata.
Ya ce ita kadai ce tilo take samarwa da maniyatan ta masauki a kusa da harami sabanin wasu hukumomin alhazai da suke yayatawa.
A na shi jawabin, Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ce wannan shi ne karo na uku da Gwamna Umar Namadi ke bai wa hukumar rancen kudi domin tare kujerun aikin hajji.
Ya ce makasudin bada rancen kudaden shi ne domin bai wa maniyatan jihar damar sauke farali.
A don haka, Labbo yace tuni hukumar ta ci gaba da rijistar maniyatan aikin Hajjin 2026 tare da bada tabbacin hukumar na ci gaba da rike kambunta wajen gabatar da aikin hajjin.
Kazalika, Alhaji Ahmed Umar Labbo, ya shawarci sauran hukumomin Alhazai su kara himma wajen biyan kudaden kujerun da aka ware musu akan lokaci.
Ya kuma yaba wa NAHCON da Gwamnatin jihar bisa hadin kai da goyon bayan da suke baiwa hukumar a kowanne lokaci.
Usman Mohammed Zaria