HausaTv:
2025-09-17@23:26:25 GMT

Jihad Islami: Ranar Quds Dama Ce Ta Hadin Kai Tsakanin Al’umma

Published: 28th, March 2025 GMT

Wakilin kungiyar gwagwarmayar Falastinawa ta Islamic Jihad a Tehran ya bayyana cewa: Ranar Qudus wata dama ce ta samar da hadin kai. A wannan rana al’ummar musulmi suna sabunta alkawarin da suka yi da Allah dangane da batun Palastinu.

Ranar Kudus tana hada kai tare da karfafa gwagwarmayar Musulunci a yankin.

Ya ci gaba da cewa, dukkanin bangarori na sun yi imanin cewa,  hanya daya tilo ta kubutar da Kudus da kuma ‘yantar da kasar Falasdinu ita ce goyon bayan Kudus da kuma tinkarar mamaye yankunan Falastinu da hakan ya hada da wannan masallaci mai alfarma da yahudawan sahyuniya suke yi.

Ranar Kudus ta duniya ita ce ranar da ke bayyana dukkan sharrin Amurka da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila, kuma a wannan rana ne ake daga tutar ‘yanci da barranta daga zalunci, inji shi.

Ya kara da cewa, Wasu daga cikin shugabannin kasashen musulmi suna nuna halin ko-in-kula ga Palastinu da kuma halin da al’ummar Palastinu suke ciki, wanda kuma shirunsu nuna goyon baya ne ga zaluncin yahudawa a kan Falastinawa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

A bayan bayan nan, an aiwatar da jerin tattaunawa tsakanin Sin da Amurka karkashin jagorancin shugabanninsu, inda aka samu kyawawan sakamakon da ya kyautata alakarsu ta tattalin arziki da cinikayya. Wannan ya nuna shawarar da a kullum Sin ke bayarwa cewa, tattaunawa ita ce mafita ga dukkan rikice-rikice, maimakon amfani da karfi.

Kasar Sin ta sha nanata cewa, babu mai samun nasara a yakin cinikayya ko haraji. Mun ga yadda aka samu hauhawar farashin kayayyaki da karuwar rashin aikin yi da faduwar darajar hannayen jari a Amurka, a lokacin da ta kaddamar da yakin haraji, wanda ya nuna cewa, maimakon cimma abun da take fata na samun fifiko, asara aka samu da lalacewar muradun kamfanoni da ’yan kasuwar kasar.

Kowace kasa tana da cikakken iko da ’yancin zabar manufofi da matakan da ya dace da ita. Da Sin ta tsaya kai da fata cewa ba za ta ba da kai a yakin haraji da Amurka ta tayar ba, hakan ya sa Amurka yin karatun ta nutsu, kuma ta tuntubi bangaren Sin domin tattaunawa.

Wadannan misalai sun nuna mana cewa, akwai hanyoyi masu sauki da inganci na samun maslaha, kuma shawarwarin da Sin take gabatarwa, su ne suka dace da yanayin duniya a yanzu. Ba dole sai kowa ya samu abun da yake so ba, amma hawa teburin sulhu da tuntubar juna tana taka muhimmiyar rawa wajen warware sabani, da lalubo inda kowane bangare zai iya saki, domin a samu mafitar da za ta karbu ga kowa. Kuma irin wannan din, shi ne burin sabuwar Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya da shugaban kasar Sin ya gabatar a baya bayan nan. Duniya ba ta bukatar mayar da hannu agogo baya ta hanyar tayar da rikice-rikice da danniya da nuna fin karfi, zamani ya sauya kuma dole salon tafiyar da harkoki ya sauya, domin dacewa da yanayin da ake ciki.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkono
  • Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
  • Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne
  • NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa