HausaTv:
2025-06-15@11:15:42 GMT

Jihad Islami: Ranar Quds Dama Ce Ta Hadin Kai Tsakanin Al’umma

Published: 28th, March 2025 GMT

Wakilin kungiyar gwagwarmayar Falastinawa ta Islamic Jihad a Tehran ya bayyana cewa: Ranar Qudus wata dama ce ta samar da hadin kai. A wannan rana al’ummar musulmi suna sabunta alkawarin da suka yi da Allah dangane da batun Palastinu.

Ranar Kudus tana hada kai tare da karfafa gwagwarmayar Musulunci a yankin.

Ya ci gaba da cewa, dukkanin bangarori na sun yi imanin cewa,  hanya daya tilo ta kubutar da Kudus da kuma ‘yantar da kasar Falasdinu ita ce goyon bayan Kudus da kuma tinkarar mamaye yankunan Falastinu da hakan ya hada da wannan masallaci mai alfarma da yahudawan sahyuniya suke yi.

Ranar Kudus ta duniya ita ce ranar da ke bayyana dukkan sharrin Amurka da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila, kuma a wannan rana ne ake daga tutar ‘yanci da barranta daga zalunci, inji shi.

Ya kara da cewa, Wasu daga cikin shugabannin kasashen musulmi suna nuna halin ko-in-kula ga Palastinu da kuma halin da al’ummar Palastinu suke ciki, wanda kuma shirunsu nuna goyon baya ne ga zaluncin yahudawa a kan Falastinawa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnan Kaduna ya bai wa sabon Sarkin Moro’a sandar mulki

Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya bai wa sabon Sarkin Moro’a, Mai Martaba Isiaku Tagwai Sambo sandar mulki, a wani biki da aka gudanar a garin Manchok da ke Ƙaramar Hukumar Kaura.

Gwamna Sani, ya bayyana cewa sarakunan gargajiya na taka muhimmiyar rawa wajen zaman lafiya, haɗin kai da kuma ci gaban al’umma.

Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai

Ya ce gwamnatinsa na bai wa sarakunan gargajiya cikakken goyon baya saboda irin rawar da suke takawa a harkar mulki da ci gaban jama’a.

“Mun jajirce wajen haɗa kan al’umma a faɗin Jihar Kaduna, ba tare da nuna bambanci ba.

“Yanzu Jihar Kaduna ta fi samun tsaro da kwanciyar hankali fiye da da. Wannan nasara ta samuwa ne sakamakon gudunmawar sarakunan gargajiya,” in ji Gwamnan.

Ya kuma buƙaci al’ummar jihar da su zauna lafiya da juna tare da yin aiki tare domin ciyar da jihar gaba.

Haka kuma, ya roƙi sarakunan da su ci gaba da jagorantar al’ummominsu cikin adalci da riƙon amana.

Bikin naɗin sarautar ya samu halartar baƙi daga sassa daban-daban, bayan rasuwar tsohon Sarkin Moro’a, Malam Tagwai Sambo, wanda ya rasu ranar 14 ga watan Yuni 2024.

Tsohon Sarkin ya rasu yana da shekaru 88, bayan mulkin shekaru 58.

Sabon Sarkin, Mai Martaba Isiaku Tagwai Sambo, ya gode wa gwamnati da al’ummar Moro’a bisa amincewar da suka yi masa.

Ya yi alƙawarin mulki cikin gaskiya da riƙon amana tare da bin doka da oda.

“Zamu haɗa kai da majalisar masarauta da kuma ɗaukacin al’umma domin tafiyar da wannan mulki yadda ya kamata,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Sanar Da Dakatar Da Tattaunawa Da Amurka A Wannan Lokaci Da Take Fuskantar Yaki Daga Isra’ila
  • Yarima Mai Jiran Gadon Saudiyya Ya Jaddada Goyon Bayan Kasarsa Ga Iran
  • An Yi Zanga-zangar Nuna Goyon Baya Ga Kin Amincewa Da Bakin Haure A Amurka 
  • Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Shaida Gamsuwa Da Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
  • An Samu Babban Canji Kan Tsarin Ciniki A Tsakanin Sin Da Afirka
  • Gwamnan Kaduna ya bai wa sabon Sarkin Moro’a sandar mulki
  • Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi
  • Hajjin 2025: Yadda Alhazan Nijeriya 7 Suka Rasa Rayukansu A Saudi Arabiya
  • Isra’ila ta kaddamar da hare-hare kan yankuna da dama na Iran ciki har da Tehran
  • Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa: Sabon Tunani Don Wanzar Da Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya