Imam sayyid Aliyul Khamina’ie Jagoran juyin juya halin musulunci na kasar Iran yayi kira ga mutanen kasar su fito kwansu da kwarkwatansu don halattar zanga-zangar ranar Kududs ta duniya a yau Jumma’a.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Jagoran yana fadar haka a wani jawabin da ya gabatar a jiya Alhahamis da yamma.

Ya kuma kara da cewa fitowar zanga-zangar ranar Kudus ta duniya alama ce ta hadin kan mutanen kasar Iran, sannan cika alkawali ne ga al-ummar kasar Falasdinu kan cewa mutanen kasar Iran ba zasu taba barinsu su, su kadai ba.

Ranar Qudus ta duniya dai, rana ce wacce Imam Khomaini (q) wanda ya kafa JMI ya ware a ko wace ranar Jumma’a ta karshe na watan Ramadan mai alfarma, na ko wace shekara, don nuna goyon bayan ga al-ummar Falasdinu wadanda ake zalunta, saboda mamayar kasarsu da aka yi. Sannan da kasancewar masallacin Al-Aksa a birnin Qudus al-kiblar musul ce da farko, wanda yake hannun yahudawan sahyoniyya a halin yanzu.

A bana wannan zanga-zangar za’a yi ta ne a dai-dai lokacinda yahudawan suke kissan kiyashi wa falasdinawa a Gaza a karkashin yakin tufanul aksa, wanda ya zuwa yanzu sun kashe falasdiyawa fiye da dubu 50 a yaynsa wasu fiye da dubub 120000 suka ji raunin..

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kungiyar Abokan Yarjejeniyar M.D.D Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ke Kai Wa Kan Iran

Kungiyar ‘Abokan Yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya’ ta yi Allah wadai da harin da haramtacciyar kasar Isra’ila ta kai kan Iran

Kasashe mambobin kungiyar aminan yarjejeniyoyin Majalisar Dinkin Duniya sun fitar da wata sanarwa ta musamman inda suka yi kakkausar suka kan wuce gona da irin haramtacciyar kasar Isra’ila ke yi kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran.

Sanarwar ta yi la’akari da harin hadin gwiwa ta sama da haramtacciyar kasar Isra’ila ta kaddamar a ranar 13 ga watan Yuni a kan wasu wurare da dama a Iran, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane da jikkata wasu daruruwa da suka hada da mata da kananan yara da masana kimiyya, matakin da ya saba wa Yarjejeniya ta Majalisar Dinkin Duniya da muhimman ka’idojin dokokin kasa da kasa.

‘Yan kungiyar sun kuma yi Allah wadai da harin ganganci kan fararen hula, da wuraren zaman jama’a, da kuma cibiyoyin nukiliyar na zaman lafiya, suna masu gargadin cewa irin wadannan ayyuka na iya haifar da watsuwar kayan aikin kimiyya da zai zama babbar barazana ga rayuwar fararen hula da muhalli.

Kungiyar ta yi kira da a tsaya tsayin daka kan amfani da karfi a kan Iran, tana mai jaddada nauyin da ke wuyan babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya na kiyaye manufofi da ka’idojin Yarjejeniyar Majalisar.

Har ila yau, ta jaddada aikin babban daraktan hukumar ta IAEA na yin Allah wadai da hare-haren da haramtacciyar kasar Isra’ila ke kaiwa kan cibiyoyin nukiliyar Iran.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kungiyar Abokan Yarjejeniyar M.D.D Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ke Kai Wa Kan Iran
  • Trump ya dakatar da kamen baƙin haure a wasu wurare na Amurka
  • An Yi Zanga-zangar Nuna Goyon Baya Ga Kin Amincewa Da Bakin Haure A Amurka 
  • Iran : harin da Isra’ila ta kai ‘ ayyana yaki’ ne_ Araghchi
  • Kamfanonin Waje Sun Ce Dole Ne Su Shiga A Dama Da Su A Cikin Kasuwar Kasar Sin
  • ICPC Ta Gurfanar Da Ma’aikacin Kotu Bisa Badakalar Naira Miliyan 9.2
  • Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Zulum ya yi wa fursunoni 66 afuwa
  • Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa: Sabon Tunani Don Wanzar Da Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya
  • Ranar Dimokuraɗiyya: Gwaman Zulum ya yi wa fursunoni 66 afuwa
  • 12 ga Yuni: Najeriya na bikin ranar dimokuraɗiyya