Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-07-31@12:33:12 GMT

Sarkin Kano Na 15 Ya Soke Hawan Daba Saboda Matsalar Tsaro

Published: 27th, March 2025 GMT

Sarkin Kano Na 15 Ya Soke Hawan Daba Saboda Matsalar Tsaro

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado Bayero, ya sanar da soke bikin Sallar Eid-el-Fitr Durbar, saboda matsalar tsaro da ya sa aka dakatar da shirye-shiryen.

 

Sarkin ya bayyana hakan ne a lokacin da yake ganawa da manema labarai a fadarsa ta karamar hukumar Nasarawa da ke Kano.

 

Ya kuma jaddada cewa zaman lafiya a tsakanin jama’a ya fi muhimmanci fiye da bikin Durbar.

 

 

Bayero ya yi nuni da cewa manyan Malaman addinin Musulunci da dattawa da masu ruwa da tsaki da ‘yan majalisarsa suka bada shawarar a soke bikin domin a samu zaman lafiya.

 

Alhaji Aminu Ado Bayero ya bukaci al’ummar Kano da su yi amfani da lokacin bukukuwan Sallah wajen ziyartar ‘yan uwa da abokan arziki, tare da shaida yadda bikin Sallah cikin kwanciyar hankali da lumana.

 

 

Ya yi addu’ar Allah ya jikanmu da rahama albarakcin wannan watan na Ramadan tare da fatan al’ummar Kano za su kasance cikin masu samun gafara da rahama.

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Sarki na 15

এছাড়াও পড়ুন:

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

Rundunar Ƴansandan jihar ba ta fitar da bayani kai tsaye ba, amma wani babban jami’i da ya nemi a ɓoye sunansa ya tabbatar da kama wanda ake zargi, tare da ce wa an tafi da shi zuwa Lokoja domin cigaba da bincike.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ZAMFARA: APC Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Dauki Don Matsalar Tsaro Na Kara Tsananta
  • Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Ziyarci Jama’a, Ya Daina Sauraron Gwamnoni — ADC
  • Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki
  • Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega
  • Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 
  • Kwamitin Aikin Hajjin 2025 Na Jihar Kano Ya Kammala Rahoton Aikinsa Na Wucin Gadi
  • Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu
  • Gwamnatin Zamfara ta amince da naɗin sabon Sarkin Katsinan Gusau
  • Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati
  • ’Yan sa-kai aƙalla 100 da jami’an tsaro 30 sun mutu a bakin aiki a Katsina —Gwamnati