Yadda Azumi Yake Sa Tsoron Allah
Published: 14th, March 2025 GMT
Takawa ta kebantattun kebantattu: sun hada duk abin alkairi na gama-garin mutane, sun hada duk abin alkairi na kebantattu sannan sun kara da nutso da zurfafawa cikin sanin Allah, ba su ganin wanin Allah, a ko da yaushe suna Fadar Allah ko suna Fadar Annabi (SAW) ko suna fadar Waliyyan Allah.
Wadannan Takawa guda Uku, Allah ya fada mana su cikin Alkur’ani yana cewa : “Ba laifi ga wadanda suka yi imani da Allah suka yi aiki mai kyau cikin abin da suka ci, idan suka yi takawa suka yi Imani, sannan suka yi wata takawa kuma suka yi Imani sannan suka yi wata takawa sannan suka yi kyautaye.
Ayar ta sauka ce lokacin da ayar haramta giya ta sauka, sai wasu daga cikin Mu’uminai shubuha ta kama su suke cewa “to yanzun ‘yan uwanmu Muminai da suka sha giya a baya fa, kuma ga shi sun mutu yanzun, to ya za a yi kenan yanzun? Sai Allah ya saukar da wannan ayar yana mai cewa ba laifi a gare su tunda sun mutu lokacin ba a haramta giyar ba.
Alhamdulillah, duk wadannan takawa guda Uku, suna daga cikin falalar Ramadana. Takawa cikin Islam, Takawa cikin Iman sai Takawa cikin Ihsan.
Azumin Ramadana, kwanaki ne kididdigaggu, wata daya ne kacal cikin watanni sha biyu, kuma Allah ya bayyana mana cewa ya san akwai marasa lafiya a cikinmu, kuma akwai matafiya a cikinmu, to sai su kididdige kwanakin da azumin ya tsere musu, su rama a wasu kwanakin.
Ayar da tagabata ta bayyana wajibcin azumin watan Ramadana a Kur’ani, sai kuma hadisi mai zuwa, zai tabbatar da wajibcin azumin watan Ramadana a Sunnah Ta Annabi (SAW).
“An gina musulunci a kan shika-shikai guda biyar: 1- Shaidawa babu wani Ubangiji da ake bautawa da gaskiya sai Allah, da Shaidawa Annabi Muhammad (SAW) Manzon Allah ne 2- Sai Tsaida Sallah, 3 – Ba da Zakka 4- Azumin watan Ramadana 5– Sai Ziyartar Dakin Allah mai girma.”
Ya zo a cikin Hadisin Dalhatu bin Abdullahi, cewa “wani Mutum ya tambayi Annabi (SAW) yana mai cewa ya Ma’aikin Allah, gaya min abin da Allah ya wajabta min na daga azumi, sai Annabi ya ce Watan Ramadana, sai Mutumin Ya kara cewa akwai wani kuma da Allah ya kara wajabta min, sai Annabi ya ce A’a sai dai in za ka yi azumin Nafila.”
Babu jayayya a duk jama’ar musulmi kan wajibcin azumin watan Ramadana.
An wajabta azumin watan Ramadana ranar Litinin, dare biyu da suka shige na watan Sha’aban bayan Hijira. Annabi (SAW) bayan ya yi Hijira zuwa Madina daga Makkah a cikin watan Rabi’ul Awwal, aka tafi zuwa Rabi’us Sani har zuwa Zulhajji, sannan aka juyo Muharram har zuwa Ramadan, a cikin shekara ta biyu kenan da Hijira aka wajabta azumin watan Ramadan.
Alhamdulillah, abin da ya gabata shi ne bayanin azumi daga littafin Allah da Sunnar Annabi Muhammad (SAW) da hadin kan al’ummar musulmi gaba daya cikin wajibcin azumi.
Nasa’i ya ruwaito, Abi Umamata ya ce “Ya Ma’aikin Allah, horar ni da wani aiki kebantacce wanda zan kebanta da shi, sai Manzon Allah (SAW) ya ce, na hore ka da yin azumi, bayan Farillah ka dinga yin na nafila, sabida shi azumi ba shi da kama cikin Ibada.” Sabida kowacce Ibada wasa zai iya shigar ta amma ban da azumi.
Wannan ya nuna alakar Ubangiji da azumi, sabida Ubangiji babu misalinsa kamar yadda azumi sh ima babu misalinsa.
Muslim ya fitar cikin Sahihinsa daga Abi Hurairata ya ce: Manzon Allah SAW Ya ce “Ubangiji Ya ce dukkan Ibada ta Dan’adam ce, sai dai azumi nawa ne, kuma ni ne zan saka masa da wannan. Don ni ya yi, to ni zan saka masa.”
Ya zo cikin Hadisi cewa “Azumi garkuwa ne (tsari ne daga Shaidan, daga wuta, daga dukkan abubuwa masu cutarwa), idan dayanku yana azumi, kar ya fadi maganar da ba ta dace ba, kar ya yi hayaniyar da ba ta dace ba, idan wani ya zage shi ko ya nemi husuma da shi, to ya ce ni mai azumi ne, na rantse da wanda ran Annabi Muhammad (SAW) ke hannunsa, warin bakin mai azumi shi ya fi kamshi ranar Lahira a wurin Ubangiji daga turaren almiski”
Muslim ya fitar cikin Sahihinsa daga Sa’adu ya ce, Manzon Allah (SAW) ya ce: “A cikin Aljannah akwai wata kofa ana kiranta da suna kofar koshi (Rayyanu), ba masu shigar ta sai masu azumi”
Mu sani yaku ‘yan uwa, Allah ya amsa mana azuminmu na Ramadana, Allah ya karfafe mu da wannan kissa cewa, Ma’anar azumi ‘kamewa ko daukakawa’. Azumi ibada ce da babu misalinta kamar yadda Ubangiji ba shi da misali, kowacce ibada cewa ake ‘na yi’ – na yi sallah, na yi zakkah, na yi sadakah na yi… amma azumi sai dai a ce ‘na bari’ – Na bar ci, na bar sha, na bar saduwa da iyali na bar… haka Rabbul izzati shi ma sai dai ka ji babu da, babu iyali, ba ya ci, ba ya sha ba, ba, ba da sauransu.
Za mu ci gaba a mako mai zuwa cikin yardar Allah.
Alhamdu Lillah.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: azumin watan Ramadana wajibcin azumi
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)
Ba tare da saninmu ba, yawancin al’ummar Afirka musamman ma naYammacin Afirka suna fama da abinda ake kira da suna irin hali ko yanayin da aka shiga sanadiyar lamarin cinikin Bayi.Bayan shekara 100 da aka yi daga shekarar 1801 zuwa 1901, an yi wani kokarin da ake yi ma kallon tamkar wani takune na yadda za’a kubuta daga irin cin fuskar da ake yi kowace rana.
Kafin dai a tsunduma sosai cikin lamarin cinikin Bayi, yana da matukar kyau a fara yin bayani kan yadda abin ya fara:Lamarin cinikin Bayi ba manufa bace ta Yammacin Turai.Duk lamarin ya zarce wani hasashen da za’a iya yi ko wani rubutun,da aka yi aka aje.Idan kuma aka duba ta bangaren nahiyar Afirka ita kanta, sha’anin cinikin Bayi ya kasance nae kafin zuwa Turawa shekaru darurra da suka gabata,lamarin kuma yana ci gaba har zuwa halin da ake ciki yanzu ,ana iya tunawa da yadda Bayin da aka saya a nahiyar Afirka ake tafiya da su ta hanyar Sahara wadda take da Yashi,ta haka ne aka fara musanyar mutane,a bada su ,sannan a amshi wasu abubuwa”.
Afirka, a matsayinta na nahiya ita ma ta dandana kudarta idan ana maganatr cinikin Bayi har zuwa shenture 14 wanda ya zarce shekara 1000 ke nan:10 ga duniyar Larabawa,sai kuma 4 ga sauran yammacin Turai. Ciniki Bayi na bangaren Larabawa ya far ne a karni na 8 hakan ta kasance ne saboda yadda addinin musulunci ya hana Musulmai daga bautar da ‘yan’uwansu. Duk da an hana hakan bukatar mutane su rika yin wasu ayyuka,don haka shi yasa Larabawa suke zuwa nahiyar Afirka domin su samu Bayin.Da farko sun tsaya ta gabas ta gabar ruwa na, Rift Balley, amma yayin da suke kasuwanci, sai suka rika yada addininsu na musulunci. Wannan ya nuan ke nan wurin da yake ana ta lamarin fataucin Bayi,ya zama yanzu babu yadda za su yi su samu Bayi daga can,don haka sannu a hankali sai suka maida akalarsu zuwa yammacin Afirka.domin idon su ya fara budewa saboda ai addinin musulunci ya hana cinikin Bayi. Wannan shi yake nuna duk yadda Larabawa suke bukatar samun ‘yan Afirka a matsayin Bayi ya zo karshe.
Abu daya wanda yake kamar sun yi kama da juna tsakaanin Larabawa da Yammacin Turai shi ne suna yin amfani ne da addini, Musulunci da Kiristanci domin su samu bakin bada dalilin da yasa suke kasuwancin mutane.A kokarin da muke na nuna yin kama da juna, sai mun yi bayani dangane da bambancin, tsakanin kasuwancin na hanyar da ake bi ta Yashi, da kuma ta wani babban Kogi da kuma na ake bi ta babban ruwa ne.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp