NAJERIYA A YAU: Halin jama’a za su shiga idan Kamfanin Kaduna Electric ya ki sauraren ma’aikatansa?
Published: 27th, February 2025 GMT
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Wutar lantarki a Najeriya ta zama ginshiƙin rayuwa da al’umma ba sa iya rayuwa ba tare da ita ba. A duk lokacin da aka ɗauke ta al’umma kan shiga matsanancin hali.
Mutane da dama sun dogara ne da wutar lantarki wajen tafiyar da harkokinsu na yau da kullum, kai har ma da na kasuwanci.
A kwanakin baya ne jihohin Kaduna, Sakkwato, Zamfara da kuma Kebbi suka fuskanci ɗaukewar wutar lantarki na tsawon kwanaki, wanda ya jefa al’ummar jihohi cikin halin ni-’yasu.
NAJERIYA A YAU: Azumin Ramadana: Ko Kun San Dabinon Da Kuke Shan Ruwa Da Shi? DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa Wasu Maza Ba Sa Son HaihuwaShirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi nazari ne kan halin da al’ummar jihohin da ke ƙarƙashin kulawar kamfanin rarraba wuta na Kaduna Electric za su shiga idan ma’aikatan kamfanin suka shiga yajin aiki.
Domin sauke shirin, latsa nan
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Lantarki Wutar Lantarki
এছাড়াও পড়ুন:
Mamakon ruwan sama ya haddasa ambaliya a Maiduguri
Ruwan sama mai ƙarfi da ya sauka da safiyar ranar Laraba a Maiduguri, Babban Birnin Jihar Borno, ya haddasa ambaliya.
Ruwan wanda ya fara sauka tun da misalin ƙarfe 5 na Asuba, ya cika tituna da gidaje musamman a unguwannin Dala, Bulunkutu, titin Damboa, filin Polo, da Federal Low Cost.
Sojoji sun daƙile hari, sun kashe mayaƙan Boko Haram 9 a Borno Shugaban hukumar zabe ta jihar Bauchi ya rasuAmbaliyar ta haifar da cikas a rayuwar jama’a, inda ruwa ya lalata dukiyoyi mutane masu tarin yawa.
Mutane da dama dun fice daga gidajensu domin neman mafaka, musamman waɗanda gidajensu ruwa ya mamaye.
Hakazalika, wasu tituna sun shafe sakamakon mamakon ruwan, lamarin da ya hana mutane fita ko komawa gidajensu da kuma yin ayyukansu na yau da kullum.
Wasu daga cikin mazauna garin sun ce ambaliyar ta tsananta ne saboda magudanan ruwa sun cika da shara irin su robobi, datti da tarkacen kayan gini.
Hakan ya hana ruwa tafiya yadda ya kamata.
Wani da ya nemi a ɓoye sunansa ya ce mafi yawan magudanan ruwan Maiduguri ba sa aiki yadda ya kamata saboda sun toshe da shara.
Ya ƙara da cewa rashin kula da tsaftar muhalli ne ya haddasa irin wannan matsala.
A halin yanzu, akwai buƙatar gwamnati ta ƙara sanya ido, ta tsaurara dokokin muhalli, da kuma wayar da kan jama’a kan muhimmancin tsaftar gari.
Har ila yau, akwai buƙatar a gyara magudanan ruwa domin gujewa irin wannan ambaliya a nan gaba.
Masana sun gargaɗi jama’a cewa ana sa ran samum mamakon ruwan sama a makonni masu zuwa.
Amma an buƙaci jama’a su ɗauki matakan kariya da kuma haɗa kai da hukumomi domin shawo kan lamarin.