Aminiya:
2025-11-02@12:29:47 GMT

An yaudari ’yan Nijeriya da suka hana Jonathan lashe Zaɓen 2015 — Ƙungiya

Published: 25th, August 2025 GMT

Wata ƙungiyar siyasa da ke goyon bayan masu fafutikar nan ta “Bring Back Our Goodluck” ta buƙaci tsohon shugaban ƙasa, Goodluck Ebele Jonathan, da ya tsaya takara a Zaɓen 2027.

Ƙungiyar ta ce a Zaɓen 2015 an yaudari ‘yan Najeriya da suka dage wajen ganin bai yi nasara ba a ƙoƙarinsa na neman wa’adi na biyu, lamarin da yanzu kowa yake nadama saboda an jefa ƙasar cikin tsanani da tsadar rayuwa da rashin tsaro.

Za a yi amfani da Hausa wajen samar da zaman lafiya — Abdulbaqi Jari Jiragen yaki sun kashe ’yan ta’adda 35 a iyakar Najeriya da Kamaru

A yayin wani taro na Arewa maso Yamma da aka gudanar ranar Lahadi a Kano, madugun ƙungiyar na ƙasa, Dokra Grema Kyari, ya bayyana cewa lokaci ya yi da Jonathan zai dawo ya “ceci Najeriya daga matsin tattalin arziƙi da rashin zaman lafiya.”

Ya zargi jam’iyyar APC da shugabanninta a wancan lokaci, ciki har da marigayi Muhammadu Buhari da Bola Ahmed Tinubu, da yi wa al’ummar Najeriya alƙawura na bogi.

Ƙungiyar ta jero dalilai huɗu da ta ce sun wajabta dawowar Jonathan da suka haɗa da samar da zaman lafiya, inganta tattalin arziƙi, shugabanci na haɗin kai da kuma kima a idon duniya.

Kyari ya yi nuni da cewa a zamanin Jonathan buhun shinkafa kilo 50 bai wuce N7,800 ba, amma yanzu yana kaiwa N80,000–N100,000.

Ya kuma ce manufofin gwamnatinsa kamar YouWin!, SURE-P da shirin bunƙasa noma sun amfani matasa da mata.

Ƙungiyar ta roƙi manyan ‘yan adawa kamar Atiku Abubakar, Rabi’u Musa Kwankwaso, Peter Obi da su haɗa kai su mara wa Jonathan baya a 2027, tana mai cewa “Zaɓen 2027 aikin ceto ne.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Zaɓen 2015 Zaɓen 2027

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya

Daga Ali Muhammad Rabi’u 

 

Gwamnatin Jihar Kwara ta kafa kwamitoci biyu domin tantance bayanan wadanda suka yi  ritaya a matakin jiha da  kananan hukumomi.

A cikin wata sanarwa da Kwamishinar Kudi ta jihar, Dakta Hauwa Nuru ta fitar, ta bayyana cewa kwamitocin za su tantance tare da tabbatar da sahihancin bayanan wadanda suka yi ritaya, domin a biya su bisa lokacin da suka bar aikin gwamnati.

A cewarta, kwamitin mutum takwas da aka kafa don kula da kudaden ritaya na matakin jiha zai kasance karkashin jagorancin Mai Duba Asusun Jiha, wato (Auditor General), yayin da wanda ke kula da matakin kananan hukumomi zai kasance karkashin Mai Duba Asusun Kananan Hukumomi.

Sanarwar ta bayyana cewa babban burin kwamitocin shi ne tabbatar da cewa an tattara bayanan masu ritaya bisa gaskiya da adalci, tare da  biyan su kai tsaye ta asusun ajiyar banki.

Ta kara da cewa, mambobin kwamitocin sun hada da wakilan tsofaffin manyan sakatarorin, kungiyar tsofaffin ma’aikata, Kungiyar Kwadago ta Najeriya (NLC), da kungiyar kwadago ta TUC, da sauransu.

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump
  • Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
  • Zaɓen Tanzania: Shugaba Samia Suluhu Hassan ta yi tazarce
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar
  • NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa
  • Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari
  • Ƙungiyar Rays Heaven ta Ƙarfafa Wayar da Kai kan Lafiyar Kwakwalwa a Kaduna
  • Karamar Hukumar Gwarzo Ta Karfafa Yaƙi Da Miyagun Kwayoyi Da Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba