Aminiya:
2025-09-18@00:42:58 GMT

An yaudari ’yan Nijeriya da suka hana Jonathan lashe Zaɓen 2015 — Ƙungiya

Published: 25th, August 2025 GMT

Wata ƙungiyar siyasa da ke goyon bayan masu fafutikar nan ta “Bring Back Our Goodluck” ta buƙaci tsohon shugaban ƙasa, Goodluck Ebele Jonathan, da ya tsaya takara a Zaɓen 2027.

Ƙungiyar ta ce a Zaɓen 2015 an yaudari ‘yan Najeriya da suka dage wajen ganin bai yi nasara ba a ƙoƙarinsa na neman wa’adi na biyu, lamarin da yanzu kowa yake nadama saboda an jefa ƙasar cikin tsanani da tsadar rayuwa da rashin tsaro.

Za a yi amfani da Hausa wajen samar da zaman lafiya — Abdulbaqi Jari Jiragen yaki sun kashe ’yan ta’adda 35 a iyakar Najeriya da Kamaru

A yayin wani taro na Arewa maso Yamma da aka gudanar ranar Lahadi a Kano, madugun ƙungiyar na ƙasa, Dokra Grema Kyari, ya bayyana cewa lokaci ya yi da Jonathan zai dawo ya “ceci Najeriya daga matsin tattalin arziƙi da rashin zaman lafiya.”

Ya zargi jam’iyyar APC da shugabanninta a wancan lokaci, ciki har da marigayi Muhammadu Buhari da Bola Ahmed Tinubu, da yi wa al’ummar Najeriya alƙawura na bogi.

Ƙungiyar ta jero dalilai huɗu da ta ce sun wajabta dawowar Jonathan da suka haɗa da samar da zaman lafiya, inganta tattalin arziƙi, shugabanci na haɗin kai da kuma kima a idon duniya.

Kyari ya yi nuni da cewa a zamanin Jonathan buhun shinkafa kilo 50 bai wuce N7,800 ba, amma yanzu yana kaiwa N80,000–N100,000.

Ya kuma ce manufofin gwamnatinsa kamar YouWin!, SURE-P da shirin bunƙasa noma sun amfani matasa da mata.

Ƙungiyar ta roƙi manyan ‘yan adawa kamar Atiku Abubakar, Rabi’u Musa Kwankwaso, Peter Obi da su haɗa kai su mara wa Jonathan baya a 2027, tana mai cewa “Zaɓen 2027 aikin ceto ne.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Zaɓen 2015 Zaɓen 2027

এছাড়াও পড়ুন:

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • Tinubu ya janye dokar ta-ɓaci da ya sanya a Ribas
  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • Baqa’i: Kowace Kasa A Duniya Tana Da Hakkin Mallakar Makamashin Nukiliya Na Zaman Lafiya
  • Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar