Sin Da Malaysia Za Su Samar Sabbin Shekaru 50 Masu Muhimmanci Na Dangantakar Kasashen Biyu
Published: 17th, April 2025 GMT
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya kai ziyarar aiki kasar Malaysia daga ranar 15 zuwa 17 ga wata. Inda bangarorin biyu suka amince da gina al’ummar Sin da Malaysia mai kyakkyawar makomar bai daya bisa manyan tsare-tsare da samar da wasu sabbin shekaru 50 masu muhimmanci na dangantakar da ke tsakanin Sin da Malaysia.
A ra’ayin Xu Liping, masani mai nazarin harkokin kudu maso gabashin Asiya na cibiyar kimiyyar zamantakewar al’umma ta kasar Sin, daukaka matsayin dangantakar da ke tsakanin Sin da Malaysia, na nufin cewa, an kara samun amincewar juna bisa manyan tsare-tsare a tsakanin kasashen biyu, kana ana ci gaba da fadada moriyar juna. Hakan zai taimaka wa hadin gwiwar da ke tsakanin kasashen biyu a fannoni daban daban zuwa wani sabon matsayi, da kafa ma’auni wajen yin hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen ASEAN, da sa kaimi ga hadin kai da hadin gwiwa a tsakanin kasashe masu tasowa, da kiyaye kwanciyar hankali da wadata a duniya. (Mai fassara: Mohammed Yahaya)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Sin da Malaysia
এছাড়াও পড়ুন:
Araghchi : Za’ayi Tattaunawar Iran da Amurka ta gaba a Rome bayan taron E3
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya ce za a yi taro karo na hudu na shawarwari tsakanin Tehran da Washington kan shirin nukiliyar Jamhuriyar Musulunci ta Iran a birnin Rome na kasar Italiya a ranar Asabar mai zuwa.
M. Araghchi ya fadawa manema labarai a gefen taron majalisar ministocin gwamnatin kasar na mako-mako yau Laraba cewa, inda ya ce taron na Rome zai kasance gabanin wani taro a ranar Juma’a na tsakanin Tehran da kasashen Turan nan uku da ake wa lakabi da E3 wato – Ingila, Faransa da kuma Jamus wadanda suka sanya hannu kan yarjejeniyar nukiliyar Iran ta 2015.
Ya ce rawar da kasashen Turai uku ke takawa ta ragu sakamakon manufofinsu a tattaunawar da aka dade ana yi, don haka a shirye muke mu gudanar da zagaye na gaba na shawarwari da su a birnin Rome.
Babban jami’in diflomasiyyar ya kara da cewa, Tehran na da burin warware batun nukiliyarta cikin lumana.”
Da aka tambaye shi game da halin da ake ciki na baya-bayan nan na kudaden da Iran ta toshe saboda takunkumin da kasashen yamma suka kakaba mata, Araghchi ya ce daskararrun kudaden na daga cikin takunkumin da ya zama dole a dagewa iran.
Kawo yanzu Iran da Amurka sun yi tattaunawa har uku ta farko a Oman, ta biyu a Italiya sai kuma wace aka gudanar a ranar Asabar data gabata a Oman.
Dukkanin bangarorin na cewa akwai fata mai kyau a jerin tattaunawar da suka gabata.