Sin Da Malaysia Za Su Samar Sabbin Shekaru 50 Masu Muhimmanci Na Dangantakar Kasashen Biyu
Published: 17th, April 2025 GMT
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya kai ziyarar aiki kasar Malaysia daga ranar 15 zuwa 17 ga wata. Inda bangarorin biyu suka amince da gina al’ummar Sin da Malaysia mai kyakkyawar makomar bai daya bisa manyan tsare-tsare da samar da wasu sabbin shekaru 50 masu muhimmanci na dangantakar da ke tsakanin Sin da Malaysia.
A ra’ayin Xu Liping, masani mai nazarin harkokin kudu maso gabashin Asiya na cibiyar kimiyyar zamantakewar al’umma ta kasar Sin, daukaka matsayin dangantakar da ke tsakanin Sin da Malaysia, na nufin cewa, an kara samun amincewar juna bisa manyan tsare-tsare a tsakanin kasashen biyu, kana ana ci gaba da fadada moriyar juna. Hakan zai taimaka wa hadin gwiwar da ke tsakanin kasashen biyu a fannoni daban daban zuwa wani sabon matsayi, da kafa ma’auni wajen yin hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen ASEAN, da sa kaimi ga hadin kai da hadin gwiwa a tsakanin kasashe masu tasowa, da kiyaye kwanciyar hankali da wadata a duniya. (Mai fassara: Mohammed Yahaya)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Sin da Malaysia
এছাড়াও পড়ুন:
Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai
Dan majalisa mai suna muhammad Mirzai ya ce; Kasashen turai sun zaku, akan su sami bayanai akan girman asarar da aka yi wa cibiyoyin Nukiliyar Iran don haka ya zama wajibi Iran din ta yi amfani da siyasar barinsu a cikin duhu.
A yayin zaman da majalisar shawarar musulunci ta Iran ta yi a yau Talata, dan majalisar ya kuma yi bayani akan kallafaffen yakin kwanaki 12, ya yi ishara akan yadda HKI ta yi amfani da kirkirarriyar fasaha da kuma wasu hanyoyi na leken asiri,amma duk da haka ta ci kasa, saboda jagoranci mai cike da fasaha na jagora, da kuma yadda al’ummar kasar ta yi tsayin daka da goyon bayan tsarin musulunci.
Haka nan kuma ya ce; Daga cikin manufofin da HKI ta Shata cewa za ta cimmawa a yayin yakin, shi ne samar da sauyi a cikin wannan yankin, shi ya sa da dama daga cikin hukumomin kasashen larabawa su ka fahimci cewa raunana Iran yana nufin raunana kasashensu.