Macron : Faransa na shirin amincewa da yankin Falasdinawa a matsayin kasa
Published: 10th, April 2025 GMT
Shugaban kasar Faransa, Emmanuel Macron, ya ce kasarsa na shirin amincewa da yankin Falasdinawa a matsayin kasa nan da watanni masu zuwa.
Ya ce hakan na iya faruwa a farkon watan Yuni nan wannan shekarar a taron Majalisar Dinkin Duniya da za a gudanar a New York.
kawo yanzu, Kasashe 147 ne suka amince da yankin na Falasdinawa a matsayin kasa mai yanci.
Kasashen Sifaniya da Ireland da Norway su ne na baya-bayan nan da suka nuna amincewarsu a watan Mayun bara da yankin na Falasdinawa a matsayin kasa mai yanci, matakin da ya fusata Isra’ila.
Kasashen duniya da kungiyoyin kasa da kasa da dama dai na ganin samar da kasashe guda biyu Falasdinu da Isra’ila shi ne gimshikin samar da zaman lafiya a yankin.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Falasdinawa a matsayin kasa
এছাড়াও পড়ুন:
Ministan man Fetur na Kasar Iran Yace Amurka Ta Kasa Hana Iran Saida Danyen Man Fetur Na Kasar
Ministan man fetur na kasar Iran Mohsen Paknejad ya bayyana cewa kasarsa zata ci gaba da saida danyen man fetur ga masu sayensa a kasashen waje duk tare da kokarin gwamnatin kasar Amurka na kara kuntatawa kasar a bangaren saida makamashin kasar ga kasashen waje.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto ministan yana fadar haka a jiya laraba bayan taron majalisar ministocin kasar a nan Tehran.
Ministan ta kara da cewa shirin Amurka na hana Iran saida danyen manta ga kasashen waje zai rugurguje kamar yadda ya rugurguje a baya. Y ace don mun rika mun gano kan zaren lalata duk wani shiri na hana mu saida danyin man ga masu sayan man kasar.
Ministan ya bayyana cewa labara ya zo masa kan cewa gwamnatin Amurka na kokarin kakabawa kasar takunkuman tattalin arziki kan sinadarin Methanol na kasar, shi ma suna aiki a kansa.
Gwamnatin Amurka ta Donal Trump tun watan Fabray run wannan shekarar ta fara wani sabin shiri na takurawa Iran, daga ciki har da maida sayar da danyen man fetur na kasar zuwa sifili.