Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-09-17@23:28:04 GMT

An Sace Dalibin Jami’ar Tarayya Birnin Kebbi

Published: 10th, April 2025 GMT

An Sace Dalibin Jami’ar Tarayya Birnin Kebbi

Rundunar ‘yan sandan jihar Kebbi, ta tabbatar da sace wani dalibi dan aji 4 na Jami’ar Tarayya ta Birnin Kebbi, mai suna Augustine Madubiya, mai shekaru 23 da haihuwa, wanda ke Sashen Tattalin Arziki zuwa inda ba a san inda aka nufa ba.

 

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, SP Nafiu Abubakar, ya shaida wa manema labarai cewa, wasu gungun ‘yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun kai farmaki gidan Istijaba Villa da ke karamar hukumar Kalgo a jihar inda suka yi garkuwa da wani dalibi a dakin kwanan dalibai a harabar jami’ar, kuma abin bakin ciki, wani Malam Siddi Hussaini, wanda ke kusa yana kiwon shanun sa, a lokacin da yake kokarin shiga tsakani, shi ma likita ya samu rauni a harin.

 

A cewarsa, yayin da yake samun rahoton, jami’in ‘yan sanda na yankin, Kalgo, ya tara tawagar jami’an tsaro hadin gwiwa zuwa wurin da lamarin ya faru, kuma a halin yanzu rundunar jami’an tsaro na ci gaba da sintiri dazuzzuka da kuma hanyoyin da ke kusa da wurin da nufin ceto wanda aka yi garkuwa da shi ba tare da jin rauni ba tare da damke wadanda suka aikata wannan ta’asa.

 

Hakazalika, a ranar Lahadin da ta gabata ne wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton ‘yan bindiga ne na Lakurawa da ke dauke da manyan muggan makamai suka kai farmaki kauyukan Tungan Taura da Tungan Ladan, a karamar hukumar Augie a jihar Kebbi, inda suka yi awon gaba da wasu shanu da ba a tantance adadinsu ba, suka kashe mutum goma sha shida.

 

SP Nafiu Abubakar ya ce, tun daga lokacin an dawo da zaman lafiya a yankunan da lamarin ya shafa kuma an fara gudanar da cikakken bincike.

 

Abdullahi Tukur

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

“Bayan karbar mukaminsa na sabon kwamandan hukumar NSCDC na jihar Kano, kwamared Bala Bodinga ya umurci jami’ansa da su sadaukar da kansu ga muhimmin aiki na tabbatar da amincin muhimman kadarori da ababen more rayuwa na kasa.

 

“Kwamandan jihar ya ba da umarnin cewa, ba dare ba rana, cikin sa’o’i 24, dole jami’an hukumar su rika yin sintiri da sanya ido domin dakile ayyukan barayi da masu aikata laifuka a lunguna da sako na jihar,” inji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
  • An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • Jami’in Kasar Yemen Ya Aike Da Sako Ga Mahalarta Taron Birnin Doha Na Kasar Qatar