Wani mamba na kungiyar Hizbullah a majalisar dokokin kasar ta Lebanon ya soki hare-haren da gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila take kai wa a kudancin kasar Lebanon da kuma keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta, yana mai jaddada cewa Amurka ce ke da alhakin kai hare-haren wuce gona da iri na sahyoniyawan.

A cewar Al-Mayadeen, mazauna kudancin kasar Lebanon sun binne gawawwakin shahidan Hizbullah 14 a garin Blida a wani gagarumin biki.

Hassan Fadlallah, wakilin kungiyar Hizbullah a majalisar dokokin kasar Lebanon ya bayyana a yayin jawabinsa cewa: Gwamnatin Sahayoniya tana cin gajiyar raunin gwamnatin Lebanon ta yi, kuma muna bukatar matsayin da ya kunshi ayyuka na zahiri, hatta a matakin siyasa da diflomasiyya.

Ya kara da cewa: “Muna kira ga gwamnatin Lebanon da kada ta yi watsi da nauyin da ke kanta, kuma idan ta dauki matakin da ya dace, to za mu tsaya tare da ita.” Makiya suna amfani da wasu muryoyi a cikin gida da ke kira ga Isra’ila da su ci gaba da kai hari a cikin Lebanon, Waɗannan ‘yan amshin shata ne kuma za su sha kunya.

Fadlallah ya jaddada cewa: Bai kamata a ci gaba da wannan lamari a kudancin Lebanon ba, kuma Amurka ce ke da alhakin kai hare-haren wuce gona da iri na gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila.

Wannan mamba na kungiyar Hizbullah ya jaddada cewa, babu batun tsro a cikin tafarkin da suke bi, kuma mutanen kudancin Lebanon sun nuna haka a aikace.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026

Gwamnatin tarayya ta umarci hukumar shirya jarrabawar WAEC da NECO da su fara amfani da cikakken tsarin amfani da Komfuta (CBT) ga dukkan jarabawar su nan da shekarar 2026. Ministan Ilimi, Dr. Tunji Alausa, ne ya bayar da wannan umarnin a ranar Litinin yayin ziyara da kuma duba yadda ake gudanar da gwaje-gwaje na CBT a cibiyoyin Bwari da kuma duba ɗakin gwajin jarrabawa JAMB a kwamfuta.

Alausa ya bayyana cewa, daga watan Mayu ko Yuni na 2026, duka ɓangarorin tambayoyin da aka saba na WAEC da NECO, na rubutu da na gwaje-gwaje, za su kasance a komfuta gaba ɗaya. Ya ƙara da cewa wannan matakin na daga cikin manufar gwamnatin na magance matsalar satar jarabawa.

Gwamnatin Kano Ta Biyawa Ɗalibai 119,903 Kudin Jarrabawar NECO Da NBAIS WAEC Ta Kwace Lasisin Makarantu 574 Sakamakon Satar Amsa

Ministan ya kuma sanar da cewa an kafa kwamitin bincike ƙarƙashin jagorancin Daraktan JAMB, Prof. Ishaq Oloyede, wanda zai duba tsarin jarabawar Nijeriya gaba ɗaya, inda aka ce sakamakon binciken zai fito nan da ƙarshen watan gobe. Alausa ya yaba da ingancin gudanar da jarabawar UTME ta 2025 da JAMB, wanda ya bayyana a matsayin “matsayi na duniya” kuma yana cika ƙa’idojin ƙasa da ƙasa.

A cikin jawabinsa, Oloyede ya bayyana cewa UTME ta 2025 tana ɗaya daga cikin mafi kyawun jarabawar da aka taɓa gudanarwa, inda ya kuma bayyana cewa duk wani zargin rashin dacewar cibiyoyin jarabawa yana buƙatar hujja mai ƙarfi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Munafunci Dodo Ya Kan Ci Mai Shi
  • Yanayin Rudani Na Tsawon Kwanaki 100 Kashedi Ne Ga Amurka
  • Nazarin CGTN: Ana Kara Bayyana Rashin Gamsuwa Da Sabuwar Gwamnatin Amurka Daga Ciki Da Wajen Kasar
  • ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
  • Shugaban Kungiyar Hizbullah Ya Abbaci Abubuwa 3 Wadanda Yakamata Kasar Ta Maida Hankali A Kansu
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jadadda Cewa: Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kan Iran Zai Fuskanci Mayar Da Martani
  • Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026
  • Lebanon:  Isra’ila Ta Kai Hari Akan Unguwar Dhahiya A Birnin Beirut
  • Kissoshin Rayuwa: Imam Hassan (a) 115
  • Kissoshin Rayuwa: Imam Al-Hassan 114