Uromi: Matar Mamaci Ta Haihu Bayan Rasuwar Mijinta, Ta Nemi Taimako
Published: 3rd, April 2025 GMT
Yanzu da ya rasu, Hauwa ta ce ba ta da tabbas kan yadda za ta yi rayuwa da ‘ya’yanta.
Lamarin mai tayar da hankali ya faru ne a ranar 27 ga watan Maris, lokacin da wasu matafiya 16 ‘yan asalin Arewacin Nijeriya suka faɗa tarkon wasu ‘yan sa-kai a Uromi, a Jihar Edo, inda suka kashe su.
Wani rahoto na musamman da gidan talabijin na News Central TV, ya bayyana halin da Hauwa ke ciki, wanda ya nuna irin tasirin da wannan lamari ya haifar.
Yanzu tana fuskantar babban ƙalubale na kula da ‘ya’yanta bakwai, tare da neman mafita game da rayuwa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Mafarauta
এছাড়াও পড়ুন:
Matashi ya rasa ransa a kan soyayya a Yobe
Wani matashi mai shekaru 20, Jibrin Saidu Lamido, ya rasa ransa bayan wani rikici a kan soyayya da ya auku ƙauyen Gurdadi da ke Ƙaramar Hukumar Yusufari a Jihar Yobe.
Rahotanni sun bayyana cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 2 na ranar Talata, lokacin da Jibrin ya je zance wajen budurwarsa Saratu Gata, mai shekaru 22, a ƙauyen Kalameri.
Majalisa ta amince Tinubu ya karɓo rancen dala biliyan 2.35 Zargin Kisan Kiristoci: ’Yan majalisar Amurka sun yi amfani da bayanai marasa tushe — GwamnatiWata majiya ta ce wani mutum da ba a san ko waye ba ya zo wajensu, tare da tafiya da budurwar sannan ya ƙalubalanci Jibrin da ya biyo su idan shi “namijin gaske ne.”
Daga nan ne rikici ya ɓarke tsakaninsu, inda wanda ake zargi ya daɓa wa Jibrin adda a wuya.
“An garzaya da shi zuwa asibitin Kumaganam amma likita ya tabbatar da mutuwarsa,” in ji majiyar ’yan sanda.
Rundunar ’yan sandan jihar ta miƙa gawar mamacin ga iyayensa don yi masa jana’iza.
Kakakin rundunar, DSP Dungus Abdulkarim, ya tabbatar da cewa suna ci gaba da neman wanda ake zargi, wanda ya tsere bayan aikata laifin.