Aminiya:
2025-06-28@10:41:21 GMT

Ɓarayin kekunan ɗinki sun shiga hannu a Borno

Published: 28th, March 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Borno, ta kama wasu matasa uku da ake zargi da satar kekunan ɗinki guda 19 a cibiyar koyon sana’a ta Dala Lawanti da ke Maiduguri.

A cewar ’yan sanda, wani mai gadi a cibiyar, Kaka Modu Mustapha, mai shekaru 34, ya haɗa baki da wasu matasa biyu – Bukar Mustapha mai shekaru 16 da Ibrahim Mohammed mai shekaru 17 – domin aikata satar a ranar 22 ga wata Maris, 2025.

ECOWAS ta gyara cibiyar magance shan miyagun ƙwayoyi a AKTH Tinubu zai sake zama shugaban ƙasa a 2027 — Akpabio

Kakakin rundunar, SP Nahum Kenneth Daso, ya ce jami’an ’yan sanda daga yankin Bulumkutu, sun samu rahoto game da satar, inda suka gudanar da bincike tare da kama waɗanda ake zargin, ciki har da mai gadin cibiyar.

Ya ce an samu nasarar ƙwato kekunan ɗinki guda shida daga cikin 19 da suka sace, yayin da ake ci gaba da bincike domin gano sauran guda 13.

SP Daso, ya buƙaci al’ummar jiharda su kasance masu kula tare da kai rahoton duk wani abun zargi ga jami’an tsaro domin daƙile aikata laifuka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Cibiyar Koyon Sana o i

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda aka kama mai garkuwa da mutane yana tsaka da cin kasuwar shanu a Neja

An kama daya daga cikin mutanen da ake zargi da yin garkuwa da mutum uku a ƙauyen Daku da ke Gwagwalada Abuja lokacin da yake tsaka da cin kasuwar shanu ta Izom da ke Guraran jihar Neja.

Rahotanni sun ce a ranar tara ga watan Yunin 2025 ce dai aka sace wasu makiyaya su biyu da wani direba a kusa da kauyen na Daku.

An sace mutanen ne lokacin da suke kan hanyarsu ta komawa gida daga kasuwar ta Izom.

’Yan sanda sun kama mutum 5 kan kisan Kanawa 2 a Benuwe Ba zan yi Tinubu ba a 2027 matukar ya canza Kashim Shettima – Sheik Jingir

Mutanen da aka sace ɗin dai a wancan lokacin sai da suka biya kudin fansa har Naira miliyan 15 kafin su shaƙi iskar ’yanci.

Wani ɗan kungiyar sintiri ta bijilan a yankin, Ishaku Daniel, ya ce an cafke wanda ake zargi da garkuwa da mutanen ne wajen misalin karfe 4:00 na yamma a kasuwar bayan daya daga cikin waɗanda ya sace ya gane shi.

Ishaku ya ce an kama mutumin ne sanye da dogayen kaya lokacin da ya shigo kasuwar domin yin sayayya.

Ya ce nan take ’yan sintirin da ke kasuwar suka cika hannu da shi, duk da cewar jama’ar gari sun so su halaka shi a nan take.

Ya kuma ce ’yan sintirin sun sami fakiti-fakitin sigari da tiramol da maganin tari da kuma wiwi a cikin buhun wanda ake zargin.

Ishaku ya ce daga bisani sun mika shi ga jami’an tsaro da suka je kasuwar daga Lambata a jihar ta Neja.

Shi ma wani jami’in tsaro da ya nemi a sakaya sunansa ya tabbatar da kama mutumin, inda ya ce tuni ya amsa laifinsa yayin da ake ci gaba da bincike a kan lamarin.

Sai dai yunkurin wakilinmu na jin ta bakin Kakakin ’yan sandan jihar ta Neja, SP Wasiu Abiodun, a kan lamarin ya ci tura har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson
  • ’Yan sanda sun kama ɓarayi 5, sun ƙwato kuɗi da makamai a Gombe
  • NDLEA ta kafa cibiyar kula da masu shaye-shaye a Yobe 
  • Tinubu ya rattaba hannu kan sababbin dokokin haraji
  • An tallafawa iyalan ‘yan sanda da Naira miliyan N13.4m a Borno
  • Yadda aka kama mai garkuwa da mutane yana tsaka da cin kasuwar shanu a Neja
  • ’Yan sanda sun kama mutum 5 kan kisan Kanawa 2 a Benuwe
  • Tinubu Zai Rattaba Hannu Kan Kudirorin Sauya Fasalin Haraji 4 A Yau Alhamis 
  • Mutane 4 Sun Mutu, 10 Sun Jikkata Yayin Da Wata Mota Ta Taka Bam A Borno
  • An ɗaure mutum 6 shekaru 120 kan satar yara a Kano