ECOWAS ta gyara cibiyar magance shan miyagun ƙwayoyi a AKTH
Published: 28th, March 2025 GMT
Ƙungiyar Raya Tattalin Arziƙin Ƙasashen Yammacin Afirka (ECOWAS), ta kammala gyara wata cibiya don kula da masu fama da shan miyagun ƙwayoyi a Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano (AKTH) da ke Kano, tare da miƙa ta ga asibitin domin amfanin jama’a.
Jami’in ECOWAS mai kula da shirin hana yawaitar shan miyagun ƙwayoyi, Dokta Daniel Akwasi Amankwaah, ya ce wannan cibiya na daga cikin ƙoƙarin ƙungiyar wajen rage yawaitar shan ƙwayoyi da kuma tabbatar da samun ingantacciyar kulawa ga masu buƙata.
A yayin bikin miƙa cibiyar, Dokta Amankwaah, ya jaddada aniyar ECOWAS na yaƙi da matsalar shan miyagun ƙwayoyi, inda ta ce duniya ta ɗauki wannan matsala a matsayin wata babbar barazana ga lafiya da zamantakewa.
Ya bayyana cewa bayanan da Hukumar Bincike kan Amfani da Miyagun Ƙwayoyi a Yammacin Afirka (WENDU), ta fitar daga 2018 zuwa 2023 sun nuna ƙaruwar masu shan miyagun ƙwayoyi a yankin, duk da ƙarancin wuraren kula da su.
Saboda haka, ECOWAS ta ƙaddamar da wani shiri tun a 2019 domin taimaka wa membobints wajen kafa ko gyara cibiyoyin kula da masu shan miyagun ƙwayoyi.
Ya zuwa yanzu, an kammala cibiyoyi takwas a ƙasashe shida, inda Najeriya ta samu guda huɗu, yayin da ake ci gaba da aikin wasu uku.
Dokta Amankwaah, ya ce kammala wannan cibiya a AKTH zai taimaka wajen kula da marasa lafiya ta hanyar dabarun kiwon lafiya, wanda zai rage illar shan miyagun ƙwayoyi tare da inganta rayuwar jama’a.
Kwamandan Hukumar NDLEA a Kano, Ahmed Idris, ya ce wannan cibiya wata babbar nasara ce a yaƙi da shan miyagun kwayoyi.
Ya yi kira da a ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin hukumomi domin cimma gagarumin nasara.
Shi ma Shugaban AKTH, Abdurrahman Abba Sheshe, ya yaba da wannan tallafi, inda ya ce cibiyar ba kawai al’ummar Kano za ta taimaka ba, har da maƙwabtan jihohi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: ECOWAS Miyagun ƙwayoyi shan miyagun ƙwayoyi
এছাড়াও পড়ুন:
Bida Poly ta kawo sojoji su kula da jarrabawar ɗalibai
Rikicin kwamitin gudanarwa da malaman Kwalejin Fasaha ta Tarayya da ke Bida (Bida Poly), ya ƙara ƙamari bayan da makarantar ta dakatar da ayyukan Kungiyar Malamai (ASUP) sannan ta kawo sojoji domin kula da jarrabawa da dalibai ke gudanarwa.
Ƙungiyar ASUP reshen kwalejin ta shiga yajin aiki mara wa’adi, domin neman a biya su alawus ɗin ƙarin aiki na watanni 18 da suka wuce.
Ƙungiyar ta umarci mambobinsu da kada su gudanar da jarrabawar zangon da ta fara ranar Litinin, 15 ga Satumba, 2025.
Wani ma’aikacin makarantar ya shaida wa wakilinmu cewa sojojin an gayyace su ne domin kare ɗalibai da wasu malamai daga shirin da ASUP ke yi na hana gudanar da jarrabawa.
’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu An kama su kan satar zinarin Naira miliyan 110 a Kebbi“Ba wai don su gudanar da jarrabawar aka kawo sojojin ba, sai don su kare ɗalibai da malamai daga duk wani cikas. Amma abin mamaki shi ne, me ya sa aka kawo sojoji maimakon ’yan sanda ko Sibil Difens?” in ji shi.
Shugaban ASUP na kwalejin, Kwamared Kolo Joshua, ya tabbatar da komawar su yajin aiki, yana mai cewa gwamnati ta yi biris da haƙƙoƙin malaman.
“Shekaru biyu ke nan muna jurewa, amma yau malaman suna bin bashin watanni 18 na kuɗin ƙarin aiki.
“Duk da tattaunawa da saƙonni da muka aika, ba a ɗauki mataki ba. Sai ma aka dakatar da ƙungiya sannan aka fara tsoratar da shugabanninmu da tambayoyi. Wannan ya jefa malaman cikin rashin kuɗi da raguwar ƙwarin guiwa,” in ji shi.
Ya ce sai dai idan gwamnati ta biya hakkokin malamai da kuma ta koma kan tattaunawa ta gaskiya ne za a samu zaman lafiya a makarantar.
Wata sanarwa da Babban Sakataren Makarantar, Hussaini Mutammad Enagi, ya fitar, ta ce an dakatar da ayyukan ƙungiyar ne bisa dalilin “fargba da kuma rahoton tsaro mai tayar da hankali.”
Sai dai jami’in hulɗa da jama’a na makarantar, Malam Abubakar Dzukogi, ya musanta cewa sojoji aka kawo.
“Na zagaya duk cibiyoyin jarrabawa, ban ga sojoji ba. ASUP ne kawai suka shiga yajin aiki, sai makaranta ta ci gaba da gudanar da jarrabawar. Wannan lamari na farar hula ne, ba na soja ba,” in ji shi.