Aminiya:
2025-11-02@21:12:49 GMT

ECOWAS ta gyara cibiyar magance shan miyagun ƙwayoyi a AKTH

Published: 28th, March 2025 GMT

Ƙungiyar Raya Tattalin Arziƙin Ƙasashen Yammacin Afirka (ECOWAS), ta kammala gyara wata cibiya don kula da masu fama da shan miyagun ƙwayoyi a Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano (AKTH) da ke Kano, tare da miƙa ta ga asibitin domin amfanin jama’a.

Jami’in ECOWAS mai kula da shirin hana yawaitar shan miyagun ƙwayoyi, Dokta Daniel Akwasi Amankwaah, ya ce wannan cibiya na daga cikin ƙoƙarin ƙungiyar wajen rage yawaitar shan ƙwayoyi da kuma tabbatar da samun ingantacciyar kulawa ga masu buƙata.

Tinubu zai sake zama shugaban ƙasa a 2027 — Akpabio ’Yan sanda sun ƙwato wa mutumin da aka sace kuɗin fansarsa a Kano

A yayin bikin miƙa cibiyar, Dokta Amankwaah, ya jaddada aniyar ECOWAS na yaƙi da matsalar shan miyagun ƙwayoyi, inda ta ce duniya ta ɗauki wannan matsala a matsayin wata babbar barazana ga lafiya da zamantakewa.

Ya bayyana cewa bayanan da Hukumar Bincike kan Amfani da Miyagun Ƙwayoyi a Yammacin Afirka (WENDU), ta fitar daga 2018 zuwa 2023 sun nuna ƙaruwar masu shan miyagun ƙwayoyi a yankin, duk da ƙarancin wuraren kula da su.

Saboda haka, ECOWAS ta ƙaddamar da wani shiri tun a 2019 domin taimaka wa membobints wajen kafa ko gyara cibiyoyin kula da masu shan miyagun ƙwayoyi.

Ya zuwa yanzu, an kammala cibiyoyi takwas a ƙasashe shida, inda Najeriya ta samu guda huɗu, yayin da ake ci gaba da aikin wasu uku.

Dokta Amankwaah, ya ce kammala wannan cibiya a AKTH zai taimaka wajen kula da marasa lafiya ta hanyar dabarun kiwon lafiya, wanda zai rage illar shan miyagun ƙwayoyi tare da inganta rayuwar jama’a.

Kwamandan Hukumar NDLEA a Kano, Ahmed Idris, ya ce wannan cibiya wata babbar nasara ce a yaƙi da shan miyagun kwayoyi.

Ya yi kira da a ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin hukumomi domin cimma gagarumin nasara.

Shi ma Shugaban AKTH, Abdurrahman Abba Sheshe, ya yaba da wannan tallafi, inda ya ce cibiyar ba kawai al’ummar Kano za ta taimaka ba, har da maƙwabtan jihohi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: ECOWAS Miyagun ƙwayoyi shan miyagun ƙwayoyi

এছাড়াও পড়ুন:

Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar October 31, 2025 Manyan Labarai NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa October 31, 2025 Manyan Labarai Yan Nijeriya Na Ɗanɗana Kuɗarsu Kan Jinkirta Cire Tallafin Mai – Sarki Sanusi October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Karamar Hukumar Bubura Ta Kai Tallafin Kayayyakin Abinci Cibiyar Gyaran Hali
  • Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba
  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi
  • Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda
  • Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari