HausaTv:
2025-04-30@18:59:13 GMT

Hukumar IAEA ta yi ishara da yiwuwar sake komawa teburin tattaunawa tare da Iran

Published: 26th, March 2025 GMT

Bayan gazawar tattaunawar da hukumar ta IAEA ta yi da Tehran, babban daraktan hukumar Rafael Grossi ya jaddada muhimmancin komawa kan teburin shawarwari nan gaba don tabbatar da cewa Iran ba ta mallaki makamin nukiliya ba.

Hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa ta ce tattaunawar da ta yi da wani babban jami’in kasar Iran a baya-bayan nan, ba a samu wani ci gaba kadan ba a cikin binciken nukiliyar da aka shafe shekaru ana yi kan kasar Iran, yana mai jaddada bukatar gaggauta warware takaddamar diflomasiyya da ke tsakanin Tehran da Washington.

A wata hira da Bloomberg babban darektan hukumar Rafael Grossi ya tabbatar da cewa nan ba da jimawa ba zai koma Tehran domin ci gaba da tattaunawa da jami’an Iran. “Muna kan wani muhimmin mataki,” in ji Grossi, yana mai cewa wadannan tattaunawa za su iya taka muhimmiyar rawa a nan gaba.

Grossi ya kara da cewa shugaban kasar Amurka Donald Trump ya aike da wasika zuwa ga jagoran ruhin Iran, wanda ke nuni da bukatar cimma fahimtar juna da ke musanta yuwuwar Iran ta mallaki makamin nukiliya.

A sa’i daya kuma, Grossi ya jaddada bukatar shugabannin kasashen duniya su yi taka-tsan-tsan da kamewa, a daidai lokacin da ake ci gaba da tafka mahawara ta kasa da kasa game da bukatar dakile makaman nukiliya.

A cikin jawabinsa, Grossi ya bayyana cewa, duniya na fuskantar kalubale guda biyu: a bangare guda, akwai batutuwan da ba a warware su daga baya ba, a daya bangaren kuma, damar da ta kunno kai na cimma wata yarjejeniya nan gaba da za ta kai ga cimma matsaya kan batun nukiliyar Iran na dogon lokaci.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Sin Za Ta Samar Da Dokar Da Ta Shafi Raya Kasa

Haka kuma za a aiwatar da dukkan abubuwan da aka dade ana yinsu cikin shirin raya kasa a hukumance.

 

Ana sa ran dokar za ta kara inganta tsare-tsaren da za su tabbatar da aiwatar da shirye-shiryen raya kasa da karfafa dacewar manufofin da suka shafi dukkan bangarorin tattalin arziki da juna. (Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araghchi : Za’ayi Tattaunawar Iran da Amurka ta gaba a Rome bayan taron E3
  • Iran ta sha alwashin ci gaba da aiwatar da manufofinta na raya dangantakarta da Nijar
  • Amurka ta sake laftawa wasu kamfaninin mai na Iran takunkumi
  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Tsara Nagartaccen Shirin Raya Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’umma Tsakanin 2026-2030
  • An Fara Baje Kolin Kayakin Da Ake Kerawa A Iran Tare Da Taron Iran Da Afirka Karo Na Uku
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Ci Gaba Da Killace Gaza Da Kashe Mutane, Laifi Ne Da Ba A Taba Yin Irinsa Ba
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Jaddada Wajabcin Komawa Kan Shirin Tsagaita Bude Wuta A Gaza
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Tattauana Da Shugaban Hukumar IAEA
  • Takht Ravanji: Iran Ba Za Ta Taba Yin Tattaunawa Akan Dakatar Da Tace Sanadarin Uranium Ba
  • Kasar Sin Za Ta Samar Da Dokar Da Ta Shafi Raya Kasa