Bam ya kashe mutum 4 da jikkata wasu a Borno
Published: 21st, March 2025 GMT
Aƙalla fasinjoji huɗu ne suka mutu yayin da wasu huɗu suka jikkata sakamakon fashewar wani bam a ƙarƙashin wata motar kasuwanci a ƙaramar hukumar Biu ta Jihar Borno.
Rundunar ’yan sandan Jihar Borno ta tabbatar ta afkuwar lamarin.
Gobara ta kashe ɗan shekara 7 a sansanin ’yan gudun hijira ’Yan bindiga sun yi garkuwa da jami’in FRSC a BenuweMajiyoyin leƙen asiri sun shaidawa Zagazola Makama cewa, lamarin ya faru ne a ranar 19 ga Maris, 2025, da misalin ƙarfe 2:30 na rana a lokacin da wata mota ƙirar Golf 3 ta Wakil Fari ta tashi daga garin Kimba zuwa garin Biu.
Bayan sun isa mahaɗar Sabon Garin Kimba, motar ta taka wata nakiya (IED), wanda ya kai ga fashewa da ta kashe fasinjoji mata uku da fasinja namiji guda nan take.
Majiyar na cewar wasu fasinjoji hudu kuma sun sami raunuka daban-dabam kuma nan da nan an kai su babban asibitin Biu don yi musu jinya.
Daga bisani likitoci sun tabbatar da mutuwar wadancan mutane huɗu sannan aka ajiye su a ɗakin ajiyar gawa na asibitin kafin a miƙa su ga ’yan uwansu don yi musu jana’iza.
Bincike na farko ya nuna cewa ’yan ta’addar ISWAP ne suka dasa waɗannan bama-bamai (IEDs) a tunanin sojoji za su taka.
Jami’an soji sun tabbatar da faruwar hakan, tare da duba ƙarin barazanar da ake fuskanta daga wadannan ‘yan ta’addan don tabbatar da tsaro ga masu amfani da hanya.
Hukumomi sun kuma ƙaddamar da gangamin wayar da kan al’umma kan haɗarin bama-bamai da ba su fashe ba, don kaucewa faruwar lamari irin ya hakan.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano
Hukumar Kula da Inshorar Lafiya ta Kasa (NHIA) a ranar Laraba ta kaddamar da shirin bayar da kulawar lafiyar gaggawa kyauta ga yara a Asibitin Koyarwa na Aminu Kano (AKTH), Kano.
Shirin, a cewar Darakta a hukumar, Dr. Salahudeen Sikiru, wani bangare ne na fadada shirin lafiyar iyaye da NHIA ke aiwatarwa zuwa ga yara masu rauni da masu bukata ta musamman.
Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkonoYa ce an fara shirin fiye da shekara ɗaya da ta gabata da nufin rage mace-macen jarirai ’yan kasa da shekaru biyar.
“Mun fara wannan shiri fiye da shekara guda da ta gabata da nufin rage mace-macen jarirai. Yanzu mun zo nan don fara na ɓangaren jarirai. Mu za mu biya kudin kulawar gaggawar yaran sannan mu tabbatar an kula da su har su samu ingantacciyar lafiya,” in ji Dr. Sikiru.
Ya kuma ce a karkashin shirin, yara da ke fama da matsalolin gaggawa kamar rashin numfashi, amosanin jini, cutar shawara da yaran da aka haifa bakwaini da ma cututtukan da ke buƙatar tiyata za su samu kulawa kyauta.
Ya ce asibitoci za su fara ba da kulawa da zarar an kawo yara, sannan su tura adadin kuɗin kula da yaran a kowanne mako ga NHIA don a biya su.
Daraktan ya kara da cewa duk yaran da ya sami kulawar gaggawar kuma, za a saka shi cikin shirin inshorar lafiya na NHIS, inda hukumar za ta ci gaba da biyan kudin inshorar don tabbatar da samun kulawar lafiya mai inganci.
“Kafin yaro ya ci gajiyar shirin, dole ne a tantance shi a a tabbatar yana da rauni da kuma ba zai iya biyan kuɗin asibiti ba. Haka nan dole ne yaro ya mallaki Lambar Shaida ta Kasa (NIN) don tabbatar da gaskiya da shigar da su cikin tsarin,” in ji shi.
Dr. Sikiru ya kuma ce, “Shiri ne kula da marasa lafiya cikin gaggawan. Da zarar sun zo, za a duba su. Asibitin sai ya turo mana jimillar adadin kudin, mu kuma mu biya.”
Ya ce wannan shiri wani bangare ne na kudurin gwamnatin tarayya na rage mace-macen jarirai da tabbatar da cewa babu yaron da ya rasa kulawar asibiti saboda rashin kudi.