Aminiya:
2025-11-25@21:18:56 GMT

’Yan bindiga sun kashe manoma 14 a Ondo

Published: 11th, March 2025 GMT

Yan bindiga sun kashe aƙalla manoma 14 yayin wani hari da suka kai yankuna huɗu a Ƙaramar Hukumar Akure ta Arewa da ke Jihar Ondo.

Yankunan da abin ya shafa — Aba Alajido, Aba Sunday, Aba Pastor da Ademekun— galibi mazaunansu ƙananan manoma ne.

Abba zai naɗa sabon Kwamishina a Kano Yadda za a samu rufin asiri da sana’ar ɗinki — Muhammad

Wata majiyar ’yan sanda, ta tabbatar da faruwar lamarin, tana mai cewa maharan ɗauke da bindigogi sun auka yankunan ne da tsakar daren ranar Asabar inda suka soma harbe-harbe kan mai uwa da wabi.

Majiyar ta ce kawo yanzu dai an tsinto gawawwaki mutum 14 yayin da ake ci gaba laluben wasu.

Wani mazaunin ɗaya daga cikin yankunan da abin ya shafa da ya buƙaci a sakaya sunansa, ya ce har kawo yanzu wasu daga mutanensu da suka tsere cikin jeji ba su dawo ba.

Ya ce tun a ranar Litinin ta makon jiya aka soma kawo musu hari, sai dai mafi munin ciki shi ne wanda ya auku a ranar Juma’a ba tare da maharan sun fuskanci wata tirjiya ba.

“Tun cikin daren ranar Juma’a suka soma kawo mana kuma duk wanda suka gani sai su buɗe masa wuta.

“Mutanenmu da dama sun gudu neman mafaka a jeji kuma ina tsammanin zuwa yanzu sun kashe mutum fiye da 40 a ƙauyukan yayin da wasu da dama sun jikkata.”

Da take zantawa da Aminiya ta wayar tarho, mai magana da yawun rundunar ’yan sandan jihar, Funmilayo Odunlami-Omisamya, ta tabbatar da faruwar lamarin.

A cewarta, an soma gudanar da bincike kan lamarin wanda kawo yanzu an tsinto gawawwakin mutum 14 a jeji.

Ta ce an tura tawagar jami’an ’yan sanda da za ta bi sawun ɓata-garin kuma tuni tarzoma ta lafa a yankin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga jihar Ondo

এছাড়াও পড়ুন:

Slot na fuskantar matsin lamba saboda rashin kataɓus a Liverpool

Kociyan ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Liverpool, Arne Slot, na fuskantar matsin lamba saboda rashin kataɓus da ƙungiyar ke fama da shi a bayan nan.

A yammacin jiya Lahadi ne Nottingham Forest ta je har filin wasa na Anfield, inda ta lallasa Liverpool da ci 3-0 a wasan mako na 12 na gasar Firimiyar Ingila.

Mayaƙan Boko Haram sun file kan mata 2 a Borno Ɗaya daga cikin ’yan matan da ISWAP ta sace a Borno ta tsere

Forest ta samu nasarar ce ta hannun Murillo a minti na 33, sai Nicolo Savona a minti na 46, sannan Morgan Gibbs-White ya ƙara na uku a minti na 78.

Sakamakon wannan rashin nasarar, Liverpool ta sauka zuwa mataki na 11 da maki 18, yayin da ita kuwa Nottingham Forest ta matsa zuwa mataki na 16 da maki 12 a teburin gasar.

Kawo yanzu dai, cikin wasanni 12 da Liverpool ta buga a gasar Firimiya, ta samu nasara a wasanni 6 ne kaɗai, sannan an doke ta a sauran 6.

Wannan mummunar rashin nasara ta sake dagula wa mai horar da ƙungiyar, Arne Slot, al’amura, musamman ganin irin matsin lambar da yake fuskanta daga magoya bayan ƙungiyar a bana.

A yanzu, hankalin mai horarwar ya koma kan wasan Champions League da za su yi da PSV a ranar Laraba.

Samun nasara a wannan wasa na iya zama abin da zai ba shi damar sauƙin numfasawa; akasin haka kuma, na iya haifar masa da babbar matsala daga mahukuntan kulob ɗin da magoya bayan da ke ƙara nuna rashin haƙuri.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hizbullah: Isra’ila na kuskure idan ta na tunanin kashe-kashen kwamandodinmu zai kawo karshen kungiyar
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 8 a Kano
  • Amarya ta yi wa angonta yankan rago bayan kwana 3 da aurensu a Katsina
  • Slot na fuskantar matsin lamba saboda rashin kataɓus a Liverpool
  • Ɗaya daga cikin ’yan matan da ISWAP ta sace a Borno ta tsere
  • ’Yan bindiga sun kashe ɗan kasuwa, sun sace matarsa a Bauchi
  • ’Yan bindiga sun kashe ’yan sanda 5 a Bauchi
  • Harin Isra’ila ya kashe mutum 5 a Kudancin Beirut
  • Najeriya : An sako mutum 38 da ‘yan bindiga suka sace a jihar Kwara_Tinubu
  • An ceto mutum 38 da aka sace a cocin Kwara — Tinubu