Aminiya:
2025-11-04@18:34:47 GMT

’Yan bindiga sun kashe manoma 14 a Ondo

Published: 11th, March 2025 GMT

Yan bindiga sun kashe aƙalla manoma 14 yayin wani hari da suka kai yankuna huɗu a Ƙaramar Hukumar Akure ta Arewa da ke Jihar Ondo.

Yankunan da abin ya shafa — Aba Alajido, Aba Sunday, Aba Pastor da Ademekun— galibi mazaunansu ƙananan manoma ne.

Abba zai naɗa sabon Kwamishina a Kano Yadda za a samu rufin asiri da sana’ar ɗinki — Muhammad

Wata majiyar ’yan sanda, ta tabbatar da faruwar lamarin, tana mai cewa maharan ɗauke da bindigogi sun auka yankunan ne da tsakar daren ranar Asabar inda suka soma harbe-harbe kan mai uwa da wabi.

Majiyar ta ce kawo yanzu dai an tsinto gawawwaki mutum 14 yayin da ake ci gaba laluben wasu.

Wani mazaunin ɗaya daga cikin yankunan da abin ya shafa da ya buƙaci a sakaya sunansa, ya ce har kawo yanzu wasu daga mutanensu da suka tsere cikin jeji ba su dawo ba.

Ya ce tun a ranar Litinin ta makon jiya aka soma kawo musu hari, sai dai mafi munin ciki shi ne wanda ya auku a ranar Juma’a ba tare da maharan sun fuskanci wata tirjiya ba.

“Tun cikin daren ranar Juma’a suka soma kawo mana kuma duk wanda suka gani sai su buɗe masa wuta.

“Mutanenmu da dama sun gudu neman mafaka a jeji kuma ina tsammanin zuwa yanzu sun kashe mutum fiye da 40 a ƙauyukan yayin da wasu da dama sun jikkata.”

Da take zantawa da Aminiya ta wayar tarho, mai magana da yawun rundunar ’yan sandan jihar, Funmilayo Odunlami-Omisamya, ta tabbatar da faruwar lamarin.

A cewarta, an soma gudanar da bincike kan lamarin wanda kawo yanzu an tsinto gawawwakin mutum 14 a jeji.

Ta ce an tura tawagar jami’an ’yan sanda da za ta bi sawun ɓata-garin kuma tuni tarzoma ta lafa a yankin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga jihar Ondo

এছাড়াও পড়ুন:

Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon

A ci gaba da keta yarjejeniyar dakatar da bude wuta da HKI ke yi a kasar labanon a jiya ma ta kai hari a kudancin kasar kuma ta yi sanadiyar  mutuwar mauta 4 tare da jikkata wasu guda 3,

Isra’ila ta kai hari da jirgin sama mara matuki kan wata mota a kauyen kafr rumman , kana kuma ta sake kai wani harin a garin kafr sir kamar yadda rahotanni suka bayyana, kuma wadannan hare haren suna zuwa ne kwanaki 3 bayan da sojojin israila suka kai samame ta kasa a kudancin labanon a yankin Nabatiya inda suka kai hari a jiya,

A ranar jumaa da ta gabata ne shugaban kasar ta labanon  joseph Aun ya nuna damuwarsa game da ci gaba da keta yarjejeniyar dakatar da bude wuta da Isra’ila ke yi, inda yayi tir da tel aviv game da irin mataken  da take dauka na karya yarjejeniyar.

A yan kwanankin nan sakatare janar din kungiyar hizbullah na kasar labanon shaikh Naim Qassem  ya jaddada cewa tsayin daka ne karfin labanon, don haka Amurka na matsin lamba ne don ganin an danneta an tauye mata yanci da raunata ta don biyan muradun gwamnati.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya November 2, 2025 Shugaban AmurkaTrump ya yi barazanar daukar matakin soji kan Najeriya November 2, 2025 Kamaru: Jagroan ‘Yan Hamayya Ya Yi Kira Da A Tsayar Da Harkoki A Fadin kasar November 1, 2025 MDD Tana Sa Ido Akan Kashe-kashen Da Ake Yi A Zaben Kasar Tanzania November 1, 2025  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada November 1, 2025 Shugaban Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini November 1, 2025 Iran ta damu da halin da ake ciki a yankin El Fasher na Sudan November 1, 2025 Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara November 1, 2025 Samia Suluhu Hassan ta lashe zaben shugaban kasa a Tanzaniya November 1, 2025 Najeriya ta musanta ikirarin Trump, na cewa Kristoci na fuskantar babbar barazana a kasar November 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sinner da Alcaraz za su buga wasan baje koli a Koriya ta Kudu
  • An kashe ’yan bindiga 19 yayin daƙile wani hari a Kano
  • Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 19, Sun Ƙwato Makamai A Kano
  • An kashe ’yan bindiga 19 yayin wani hari a Kano
  • Marasa Lafiya A Nasarawa Sun Koka Game Da Yajin Aikin Likitoci
  • NAJERIYA A YAU: Ko Kawo Dakarun Kasar Amurka Zai Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Najeriya?
  • Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Wasu Yan Ta’adda Sun Kashe Dakarun Sa Kai 2 A Kudu Maso Gabashin Iran
  • Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon