’Yan bindiga sun kashe manoma 14 a Ondo
Published: 11th, March 2025 GMT
’Yan bindiga sun kashe aƙalla manoma 14 yayin wani hari da suka kai yankuna huɗu a Ƙaramar Hukumar Akure ta Arewa da ke Jihar Ondo.
Yankunan da abin ya shafa — Aba Alajido, Aba Sunday, Aba Pastor da Ademekun— galibi mazaunansu ƙananan manoma ne.
Abba zai naɗa sabon Kwamishina a Kano Yadda za a samu rufin asiri da sana’ar ɗinki — MuhammadWata majiyar ’yan sanda, ta tabbatar da faruwar lamarin, tana mai cewa maharan ɗauke da bindigogi sun auka yankunan ne da tsakar daren ranar Asabar inda suka soma harbe-harbe kan mai uwa da wabi.
Majiyar ta ce kawo yanzu dai an tsinto gawawwaki mutum 14 yayin da ake ci gaba laluben wasu.
Wani mazaunin ɗaya daga cikin yankunan da abin ya shafa da ya buƙaci a sakaya sunansa, ya ce har kawo yanzu wasu daga mutanensu da suka tsere cikin jeji ba su dawo ba.
Ya ce tun a ranar Litinin ta makon jiya aka soma kawo musu hari, sai dai mafi munin ciki shi ne wanda ya auku a ranar Juma’a ba tare da maharan sun fuskanci wata tirjiya ba.
“Tun cikin daren ranar Juma’a suka soma kawo mana kuma duk wanda suka gani sai su buɗe masa wuta.
“Mutanenmu da dama sun gudu neman mafaka a jeji kuma ina tsammanin zuwa yanzu sun kashe mutum fiye da 40 a ƙauyukan yayin da wasu da dama sun jikkata.”
Da take zantawa da Aminiya ta wayar tarho, mai magana da yawun rundunar ’yan sandan jihar, Funmilayo Odunlami-Omisamya, ta tabbatar da faruwar lamarin.
A cewarta, an soma gudanar da bincike kan lamarin wanda kawo yanzu an tsinto gawawwakin mutum 14 a jeji.
Ta ce an tura tawagar jami’an ’yan sanda da za ta bi sawun ɓata-garin kuma tuni tarzoma ta lafa a yankin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga jihar Ondo
এছাড়াও পড়ুন:
Mutum 21 sun rasu a hatsarin mota a kan hanyar Zariya–Kano
Aƙalla mutum 21 ne suka rasu a wani mummunan hatsarin mota da ya auku a kan babban titin Zariya zuwa Kano.
Hukumar Kiyaye Haɗura ta Ƙasa (FRSC), reshen jihar ce ta tabbatar aukuwar hatsarin.
Hatsarin ya auku ne da misalin ƙarfe 8:23 na safe a unguwar Kasuwar Dogo da ke yankin Dakatsalle.
Zulum ya musanta shirin ficewa daga APC Gwamna ya gargaɗi sarakuna kan mamaye filayen kiwo a GombeHatsarin ya rutsa da wata babbar mota ƙirar DAF mai lambar GWL 422 ZE da kuma motar ɗaukar fasinjoji ƙirar Toyota Hummer mai lambar KMC 171 YM.
FRSC, ta ce bincike ya nuna cewa direban motar fasinjojin ne ya karya doka ta hanyar bin hanyar da ba ta dace ba, wanda hakan ya sa suka yi karo da babbar motar.
Bayan aukuwar hatsarin, motocin biyu sun kama da wuta, inda mutane da dama suka ƙone ƙurmus.
Kwamandan FRSC na Kano, MB Bature, ya ce jami’ansu sun isa wajen cikin gaggawa bayan samun rahoto.
Sun kuma kira ma’aikatan kashe gobara na jihar da na tarayya domin kashe gobarar da kuma ceto waɗanda hatsarin ya rutsa da su.
Mai magana da yawun FRSC, Abdullahi Labaran, ya ce: “Mutum 24 ne hatsarin ya rutsa da su. Abin takaici, 21 sun rasu, yayin da uku suka jikkata.”
Gawarwakin da suka ƙone an kai su ɗakin ajiye gawa na Asibitin Nassarawa da ke Kano, yayin da waɗanda suka jikkata ke samun kulawa a Asibitin Gwamnati da ke Garun Malam.
Bayan haka, jami’an FRSC tare da taimakon ’yan sanda sun ɗauke motocin da suka tare hanya domin sauƙaƙa zirga-zirgar ababen hawa a titin.
Kwamanda Bature, ya bayyana alhininsa kan wannan mummunan lamari, tare da miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan waɗanda suka rasu.
Ya kuma yi wa waɗanda suka jikkata addu’ar samun sauƙi.
Ya kuma yi amfani da wannan dama wajen jan hankalin direbobi su guji karya doka; kamar bin hanya ba daidai ba da tuƙin ganganci, wanda hakan ke haddasa haɗura.
“Wannan lamari abin takaici ne wanda ke nuna muhimmancin bin ƙa’idojin hanya. Mafi yawan haɗura za a iya kauce musu idan direbobi za su kiyaye doka,” in ji Bature.
Ya kuma buƙaci direbobi, musamman na motocin haya, da su guji gudu fiye da ƙima da ganganci a hanya, wanda a cewarsa shi ne babban dalilin da ke haddasa haɗura da asarar rayuka.
Ga hotunan yadda hatsarin ya auku: