’Yan bindiga sun kashe manoma 14 a Ondo
Published: 11th, March 2025 GMT
’Yan bindiga sun kashe aƙalla manoma 14 yayin wani hari da suka kai yankuna huɗu a Ƙaramar Hukumar Akure ta Arewa da ke Jihar Ondo.
Yankunan da abin ya shafa — Aba Alajido, Aba Sunday, Aba Pastor da Ademekun— galibi mazaunansu ƙananan manoma ne.
Abba zai naɗa sabon Kwamishina a Kano Yadda za a samu rufin asiri da sana’ar ɗinki — MuhammadWata majiyar ’yan sanda, ta tabbatar da faruwar lamarin, tana mai cewa maharan ɗauke da bindigogi sun auka yankunan ne da tsakar daren ranar Asabar inda suka soma harbe-harbe kan mai uwa da wabi.
Majiyar ta ce kawo yanzu dai an tsinto gawawwaki mutum 14 yayin da ake ci gaba laluben wasu.
Wani mazaunin ɗaya daga cikin yankunan da abin ya shafa da ya buƙaci a sakaya sunansa, ya ce har kawo yanzu wasu daga mutanensu da suka tsere cikin jeji ba su dawo ba.
Ya ce tun a ranar Litinin ta makon jiya aka soma kawo musu hari, sai dai mafi munin ciki shi ne wanda ya auku a ranar Juma’a ba tare da maharan sun fuskanci wata tirjiya ba.
“Tun cikin daren ranar Juma’a suka soma kawo mana kuma duk wanda suka gani sai su buɗe masa wuta.
“Mutanenmu da dama sun gudu neman mafaka a jeji kuma ina tsammanin zuwa yanzu sun kashe mutum fiye da 40 a ƙauyukan yayin da wasu da dama sun jikkata.”
Da take zantawa da Aminiya ta wayar tarho, mai magana da yawun rundunar ’yan sandan jihar, Funmilayo Odunlami-Omisamya, ta tabbatar da faruwar lamarin.
A cewarta, an soma gudanar da bincike kan lamarin wanda kawo yanzu an tsinto gawawwakin mutum 14 a jeji.
Ta ce an tura tawagar jami’an ’yan sanda da za ta bi sawun ɓata-garin kuma tuni tarzoma ta lafa a yankin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga jihar Ondo
এছাড়াও পড়ুন:
Jami’an tsaro sun kama masu garkuwa da mutane 7 a Gombe
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe, tare da haɗin gwiwar maharba, sun samu nasarar tarwatsa gungun masu garkuwa da mutane, tare da kama mutum bakwai da ake zargi da aikata laifuka a Jihohin Gombe, Bauchi, Yobe da Adamawa.
Rundunar ta samu nasarar ne bayan kama Abdullahi Ibrahim, mai shekaru 40 daga ƙauyen Tilde a Funakaye, a ranar 23 ga watan Nuwamba 2025.
An harbe manomi saboda rikici kan filin kiwo a Borno DSS ta kama likitan da ke duba ’yan bindiga a dazukan KwaraAn kama shi ne bayan samun bayanan sirri kan hulɗa da masu satar shanu.
Abdullahi, ya amsa cewa yana da hannu a garkuwa da mutane tare da bayyana sunayen waɗanda suke aikata laifin tare.
A cewar kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi, jami’an Operation Hattara tare da maharba ne suka kai samame maɓoyarsu a ranar 28 ga watan Nuwamba 2025, inda suka kama mutum shida bayan yin artabu.
Waɗanda aka kama sun haɗa da; Usman Mohammed, Hussain Idris, Adamu Tukur, Ya’u Abdullahi, Ali Umar, Hassan Usman da Abdullahi Ibrahim.
Rundunar ta ce waɗanda ake zargin sun amsa cewa suna da hannu a garkuwa da mutane tare karɓar kuɗin fansa kusan Naira miliyan 150.
Jami’an sun shiga dajin Gadam, inda suka samu bindiga ƙirar GPMG mai jigida guda ɗaya da harsasai takwas bayan wata musayar wuta da suka yi wasu ’yan ta’adda da suka tsere.
Haka kuma an gano suna da hannu wajen garkuwa da wani mutum a ƙauyen Barderi a Akko, a ranar 15 ga watan Janairun 2025.
Sun tsare mutumin na tsawon makonni biyu kafin karɓar Naira miliyan 15 a matsayin kuɗin fansa.
DSP Buhari, ya ce ana cigaba da bincike, kuma za a gurfanar da su a kotu.
Ya roƙi jama’a da su ci gaba da bai wa rundunar sahihan bayanai domin inganta harkokin tsaro.
Rundunar ‘Yan Sandan Gombe ta ce za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin al’umma a faɗin jihar.