Aminiya:
2025-12-02@13:35:57 GMT

’Yan bindiga sun kashe manoma 14 a Ondo

Published: 11th, March 2025 GMT

Yan bindiga sun kashe aƙalla manoma 14 yayin wani hari da suka kai yankuna huɗu a Ƙaramar Hukumar Akure ta Arewa da ke Jihar Ondo.

Yankunan da abin ya shafa — Aba Alajido, Aba Sunday, Aba Pastor da Ademekun— galibi mazaunansu ƙananan manoma ne.

Abba zai naɗa sabon Kwamishina a Kano Yadda za a samu rufin asiri da sana’ar ɗinki — Muhammad

Wata majiyar ’yan sanda, ta tabbatar da faruwar lamarin, tana mai cewa maharan ɗauke da bindigogi sun auka yankunan ne da tsakar daren ranar Asabar inda suka soma harbe-harbe kan mai uwa da wabi.

Majiyar ta ce kawo yanzu dai an tsinto gawawwaki mutum 14 yayin da ake ci gaba laluben wasu.

Wani mazaunin ɗaya daga cikin yankunan da abin ya shafa da ya buƙaci a sakaya sunansa, ya ce har kawo yanzu wasu daga mutanensu da suka tsere cikin jeji ba su dawo ba.

Ya ce tun a ranar Litinin ta makon jiya aka soma kawo musu hari, sai dai mafi munin ciki shi ne wanda ya auku a ranar Juma’a ba tare da maharan sun fuskanci wata tirjiya ba.

“Tun cikin daren ranar Juma’a suka soma kawo mana kuma duk wanda suka gani sai su buɗe masa wuta.

“Mutanenmu da dama sun gudu neman mafaka a jeji kuma ina tsammanin zuwa yanzu sun kashe mutum fiye da 40 a ƙauyukan yayin da wasu da dama sun jikkata.”

Da take zantawa da Aminiya ta wayar tarho, mai magana da yawun rundunar ’yan sandan jihar, Funmilayo Odunlami-Omisamya, ta tabbatar da faruwar lamarin.

A cewarta, an soma gudanar da bincike kan lamarin wanda kawo yanzu an tsinto gawawwakin mutum 14 a jeji.

Ta ce an tura tawagar jami’an ’yan sanda da za ta bi sawun ɓata-garin kuma tuni tarzoma ta lafa a yankin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga jihar Ondo

এছাড়াও পড়ুন:

Pezeshkian: Makiya na neman kawo cikas ga ci gaban kasashen Musulmi

Pars Today – Shugaban Iran, a wata ganawa da Ministan Harkokin Wajen Turkiyya, ya ce a lokacin da maƙiyan ƙasashen Musulmi ke neman ƙara matsin lamba, ana sa ran ƙasashen Musulunci za su sauƙaƙa wa junansu yanayi da kuma guje wa matsaloli masu sarkakiya.

Masoud Pezeshkian, Shugaban Iran, a ranar Lahadi da yamma a ganawarsa da Hakan Fidan, Ministan Harkokin Wajen Turkiyya, ya yi magana game da tarihin dangantaka tsakanin ƙasashen biyu, al’adu, da kuma ‘yan’uwa. Ya bayyana waɗannan alaƙar a matsayin mai zurfi, na gaskiya, kuma cike da fa’idodi masu yawa na ci gaba. Ya ƙara da cewa idan ƙasashen Musulunci suka yi aiki da niyya ɗaya bisa haɗin kai, haɗin kai, da musayar gogewa, babu wani iko da zai iya haifar da matsala ga ƙasashen Musulmi.

A cewar Pars Today, Pezeshkian ya jaddada buƙatar ƙarfafa dangantaka da haɗuwar dabaru tsakanin ƙasashen Musulunci. Ya dauki wani bangare na rikicin da ke faruwa a yankin a matsayin sakamakon makirci da kuma rura wutar rarrabuwar kawuna daga wasu masu shiga tsakani, yana mai cewa: “Manufar wadannan kungiyoyi ita ce sanya manufofinsu da manufofinsu marasa kyau a yankin da kuma haifar da cikas ga ci gaba da ci gaban kasashen Musulunci.”

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Shugaban venuzuwela Ya Gargadi Amurka Game Da Kokarin Da Take yi Na Karbe Ikon Kula Da Rijiyoyin Mai Na Kasar December 1, 2025 Zanga zanga Ta Barke A Isra’ila Yayin Da Natanyaho Ke Neman Afuwa Kan Batun Cin Hanci Da Rashawa December 1, 2025 Mataimakin Ministan Harkokin Wajen Kasar Saudiya Ya Gana Da Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran. December 1, 2025 Lebanon: Sakon Kungiyar Hizbullah Ga Paparoma December 1, 2025 Ireland Ta Sauya Sunan Wurin Shakatawa Daga Na Shugaban  “Isra’ila” Zuwa Na Shahidiyar Falasdinu November 30, 2025  Gaza: Sau 590 “Isra’ila” Ta Keta Tsagaiwa Wutar Yaki November 30, 2025 Washington Post: Shirin Trump Na Kai Sojojin Gaza Yana Fuskantar Matsala November 30, 2025 MDD: Kasar Somaliya Tana Fuskantar Mawuyacin Yanayi Saboda Fari November 30, 2025 An Yi Ganawa A Tsakanin Ministocin Harkokin Wajen Iran Da Turkiya November 30, 2025 An yi gangami a fadin duniya a zagayowar ranar Falasdinu November 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An yi garkuwa da manoma 11 a Kudancin Kaduna
  • ’Yan ta’adda sun kashe ɗan sanda a gidan DPO a Jigawa
  • An kama ’yan bindiga 4 a Kano
  • ’Yan bindiga sun sace fasto da matarsa  masu ibada a Kogi 
  • Pezeshkian: Makiya na neman kawo cikas ga ci gaban kasashen Musulmi
  • Zanga zanga Ta Barke A Isra’ila Yayin Da Natanyaho Ke Neman Afuwa Kan Batun Cin Hanci Da Rashawa
  • ’Yan bindiga sun sace amarya da ƙawenta 14 a Sakkwato
  • Mutum 6 sun jikkata a rikici manoma da makiyaya a Jigawa
  • Sojoji sun ceto mutum 7 da ’yan bindiga suka sace a Kano
  • ’Yan bindiga sun kashe tsohuwa, sun sace mutum 3 a Kano