’Yan bindiga sun kashe manoma 14 a Ondo
Published: 11th, March 2025 GMT
’Yan bindiga sun kashe aƙalla manoma 14 yayin wani hari da suka kai yankuna huɗu a Ƙaramar Hukumar Akure ta Arewa da ke Jihar Ondo.
Yankunan da abin ya shafa — Aba Alajido, Aba Sunday, Aba Pastor da Ademekun— galibi mazaunansu ƙananan manoma ne.
Abba zai naɗa sabon Kwamishina a Kano Yadda za a samu rufin asiri da sana’ar ɗinki — MuhammadWata majiyar ’yan sanda, ta tabbatar da faruwar lamarin, tana mai cewa maharan ɗauke da bindigogi sun auka yankunan ne da tsakar daren ranar Asabar inda suka soma harbe-harbe kan mai uwa da wabi.
Majiyar ta ce kawo yanzu dai an tsinto gawawwaki mutum 14 yayin da ake ci gaba laluben wasu.
Wani mazaunin ɗaya daga cikin yankunan da abin ya shafa da ya buƙaci a sakaya sunansa, ya ce har kawo yanzu wasu daga mutanensu da suka tsere cikin jeji ba su dawo ba.
Ya ce tun a ranar Litinin ta makon jiya aka soma kawo musu hari, sai dai mafi munin ciki shi ne wanda ya auku a ranar Juma’a ba tare da maharan sun fuskanci wata tirjiya ba.
“Tun cikin daren ranar Juma’a suka soma kawo mana kuma duk wanda suka gani sai su buɗe masa wuta.
“Mutanenmu da dama sun gudu neman mafaka a jeji kuma ina tsammanin zuwa yanzu sun kashe mutum fiye da 40 a ƙauyukan yayin da wasu da dama sun jikkata.”
Da take zantawa da Aminiya ta wayar tarho, mai magana da yawun rundunar ’yan sandan jihar, Funmilayo Odunlami-Omisamya, ta tabbatar da faruwar lamarin.
A cewarta, an soma gudanar da bincike kan lamarin wanda kawo yanzu an tsinto gawawwakin mutum 14 a jeji.
Ta ce an tura tawagar jami’an ’yan sanda da za ta bi sawun ɓata-garin kuma tuni tarzoma ta lafa a yankin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga jihar Ondo
এছাড়াও পড়ুন:
Muna buƙatar taimakon ƙasashen waje kan tsaro a Najeriya — Obasanjo
Tsohon Shugaban Ƙasa, Olusegun Obasanjo, ya ce Najeriya na buƙatar taimakon ƙasashen waje don dakatar da kashe-kashe da rashin tsaro, domin gwamnati ta gaza kare al’umma.
Ya bayyana haka ne a wani taro da ya gudana Jihar Filato, inda ya ce a ci gaba ya kawo fasahar da za a iya gano masu aikata laifi, amma ta gaza yin hakan.
Yadda aka horar da mata 100 sana’o’in dogaro da kai a Gombe Yadda ’yan mata ke kuɗancewa da kasuwancin fara a KanoObasanjo, ya yi gargaɗin cewa ana kashe ’yan Najeriya ba tare da la’akari da addini ko ƙabilanci ba, don haka gwamnati ta gaggauta ɗaukar mataki.
Ya ce idan gwamnati ta kasa kare jama’a, ’yan ƙasa na da damar neman taimakon ƙasashen duniya.
Ya soki masu kare kashe-kashen da ake yi, inda ya bayyana cewa rayuwar kowanne ɗan Najeriya na da muhimmanci.
Obasanjo, ya kuma tambayi dalilin da ya sa gwamnati ke tattaunawa ko biyan kuɗin ’yan bindiga kuɗin fansa, inda ya ce hakan na ƙara taɓarɓarewar lamarin.
Ya kira ’yan Najeriya da su haɗa kai domin tabbatar da zaman lafiya, tare da tabbatar da cewa kowa na rayuwa ba tare da fargaba ba.
Gwamnan Jihar Filato, Caleb Mutfwang, shi ma ya yi jawabi a wajen taron.
Ya ce al’ummar jihar dole su haɗa kai su daina abubuwan da za su raba su.
Mutfwang, ya buƙaci jama’a su yi aiki tare domin jihar ta ci gaba da kuma shawo kan matsalolin tsaro.