HausaTv:
2025-09-18@23:37:27 GMT

Sharhin Bayan Labarai: Kasashen Afirka Sun Kori Sojojin Faransa Daga Kasashensu

Published: 9th, March 2025 GMT

Assalamu alaikum masu sauraro sharhin bayan labarammu zai yi magana dangane da ‘Korar sojoijin Faransa daga kasa ta 7 a yammacin Afirka tare bukatar’ macron ya nemi uzurin kasashen’ wanda ni tahir amin zamn karanta.

///…Madalla, Bayan da kasashen Mali da Burkina faso, da Nigerda Ivory Coast suke kori sojojin Faransa daga kasashensu, a yanzun kuma kasar Senegal ta bada sanarwan korar sojojin kasar Faransa daga kasar.

Tun bayan juyin mulkin da sojoji suka yi a kasar Mali da kuma korar sojojin kasashen waje, daga cikin har da sojojin kasar Faransa da kuma na Majalisar dinkin duniya daga kasar, daya bayan daya kasashen yankin yammacin Afirka kuma tsoffin kasashen da Faransa tayiwa mulkin mallaka suka suka fara korar sojojin faransa daga kasashensu.

Bayan Burkiya Faso sai Jumhuriyar Niger, sannan Ivory Coast sannan yau kuma Senegal. Wannan yana daga cikin sauye-sauyen  da suke faruwa a kasashen yammacin Afirka a cikin yan sheakrun da suka gabata, wanda kuma yake nuna yadda kasashen da aka yiwa mulkin mallaka a wannan yankin, suke kin wadanda suka yi masu mulkin mallaka, hatta bayan sun basu abinda suka kira yenci.

A zahiri dukkan wadannan kasashe, babu ko da guda wacce take da wani cikin gaban a zo a gani, ta ko wani bangare, fiye da shekaru 60 da kasar faransa tace ba basu yencin kai, ba abinda take yi sai kwasar dokokiyoyin wadannan kasashe zuwa kasashensu.

Misali shi ne, an ce kasha 20% na ton 88,200 na sinadarim Uranium da ya shiga kasar faransa a cikin shekaru 10 da suka gabata ya fito daga Jumhuriyar Niger ne. A kasar Mali kasar faransa tana fitar da ton ton na gola-golan zuwa kasar faransa, amma ba zaka taba ganin wata ci gaba a kasar ba.

Kamfanin dillancin labaran Pars today ya nakalto daga tashar talabijin ta Euronews yana cewa ofishin jakadancin kasar Faransa na cewa a ranar Lahadi 9 ga watan Maris, sojojin kasar Faransa sun mika sansanonin sojoji guda biyu da ke hannunsa ga sojojin kasar ta Senegal.

Kafin haka dai a ranar 2 ga watan Fabrayrun shekara ta 2025 ne kasashen biyu suka kafa kwamitin hadin guiwa na kula da shirin ficewar sojojin faransa daga kasar.

Sai kuma kasar Ivory Coast inda sojojin Faransa suka mika sansanin sojojin kasar tilo a kasar Ivory coast ga sojojin kasar a ranar 20 ga watan Fabrayru. Ministan harkokin wajen kasar Faransa Sepostine Lakunu da tokwaransa na kasar Ivory Coast

Tane Perohimi Watara ne, suka rattaba hannu kan takardun ficewar sojojin kasar faransa, daga kasar.

Kamfanin dillancin labaran Isna na kasar Iran ya bayyana cewa, sojojin kasar Faransa 400 suke zaune a sansanin sojojin kasar. Sannan kwamandan sojojin Ivory Coast ne ya bada sanarwan kawo karshen zaman sojojin kasar Faransa a kasar a wani biki bamusamman da aka gudanar a babban birnin kasar a ranar 19 ga watan Fabrairun shekara ta 2023.

Labarin ya ce a bikinne aka sauke tutar kasar Faransam sannan aka sane shi sai kuma aka daga tutar Burkina faso a inda aka sauko da na faransa. 

Amma kafin haka sojojin kasar Faransa sun fice daga kasar Mali ne a ranar 20 ga watan Augustan shekara ta 2022m bayan shekaru 9 da shiga kasar da sunan tabbatar da zaman lafiya.

Komandan rundunar sojojin kasar faransa a Mali, ya bada sanarwan aikin rundunarsa wacce ake kira Barkhane a wannan ranar, inda suka ratsa ta Niger suka kuma fice daga yankin kwata-kwata.

A niger dai sojojin Faransa 1500 ne suke zauna a birnin Yemai, kafin su fice a ranar 22 ga watan Decemban shekara ta 2023. Haka ma kasar Chadi sojojin Faransa sun fice daga wani sansaninsu a birnin Njamena ne, a ranar 30 ga watan Jenerun shekara ta 2024.

Ya zuwa yanzu dai sojojin Faransa sun fice daga mafi yawan kasashen da take zama a cikin, sai kasar Njibuti, inda take da sojojin 1,500 da kum Gabon inda take da sojoji 350.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: sojojin kasar faransa sojojin kasar Faransa sojojin Faransa daga sojojin faransa daga Faransa sun Ivory Coast

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Gwgawarmaya Sun Kashe Sojojin HKi 4 A Gaza

Kafafen watsa labarun HKI sun ambaci cewa 4 daga cikin sojojinsu na mamaya sun halaka a sanadiyyar fashewar wata nakiya da aka dasa wacce ta tashi da daya daga cikin motocinsu a Gaza.

Majiyar ‘yan sahayoniyar ta ce,baya ga sojojin 4 da su ka halaka a yau Alhamis, an kuma samu wasu 8 da su ka jikkata lokacin da motar Hommer ta daukar sojoji da aka dasawa nakiya ta fashe da su.

Kafafen watsa labarun na ‘yan sahayoniya sun bayyana abinda ya faru da cewa: Yana da tsananin ciwo”, sannan kuma su ka kara da cewa, labarin ya faru ne a yankin da ake dauka cewa yana da aminci.

A wani gefen, kungiyar ” Kata’ibul-Mujahidin” ta sanar a yau Alhamis cewa; mayakanta sun harbi tankar yaki ta ” Mirkava” da makamin “Sa’ir” a unguwar “Zaytun”, ya kuma same ta da kyau.

Tun daga lokacin da sojojin mamaya su ka fara kai sabbin hare-hare da zummar sake mamaye yankin Gaza, ‘yan gwgawarmaya suke kara kaimi wajen kai musu hare-hare.

Yakin da HKI ta shelanta akan Gaza ya cika kwanaki 712, wanda yake cike da kisan kiyashi da na kare dangi.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka  An Halaka Sojojin HKI Biyu Ta Hanyar Sukarsu Da Wuka A Kusa Da Iyakar Jordan September 18, 2025 Husi: Kai Wa Kasar Katar Hari Gargadi Ne Ga Al’ummar Musulmi September 18, 2025 Shugaban Kasar Iran Ya bayyana Yadda Hadin Gwiwa Tsakanin Iran Da Rasha Ya Kawo Ci Gaba Tsakaninsu September 18, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce: Iran Ta Sauke Hakkin Da Ya Hau Kanta Sauran Bangaren Turai September 18, 2025 Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Ce: Masu Goyon Bayan Isra’ila Suna Da Hannu A Laifukanta September 18, 2025 Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Cika Kwanaki 713 Suna Kisan Kiyashi A Zirin Gaza September 18, 2025 Harin Makami Mai Linzami Yemen Ya Tilastawa Jirgin Fira Ministan Gwamnatin Isra’ila Saukar Gaggawa September 18, 2025 Eslami: Dole ne IAEA ta zama mai cikakken ‘yancin cin gashin kai September 18, 2025 Rahoto: An yi tattaunawa mai tsawo tsakanin Syria da Isra’ila a Landan September 18, 2025 Sheikh Qassem: Harin Pager jarabawa ce wadda ta kara wa masu gwagwarmaya kwarin gwiwa September 18, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang
  • ‘Yan Gwgawarmaya Sun Kashe Sojojin HKi 4 A Gaza
  • Yadda jariri ya rasu a bayan mahaifiyarsa yayin tsere wa harin ’yan bindiga a Neja
  • Pezeshkian: Iran da Masar suna da tsohon tarihi a duniya
  • ’Yan bindiga sun sako ma’auratan da suka sace a Katsina bayan biyan N50m
  • Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
  • Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
  • Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
  • Pezeshkian: Saudiyya Na Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Samar Da Hadin Kan Kasashen Musulmi
  • Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya tare da kiyaye hadin kai