Jihar Jigawa Ta Yi Garambawul Ga Dokar Bada Tallafi Ga Masu Bukata Ta Musamman
Published: 6th, March 2025 GMT
Majalisar Dokokin jihar Jigawa ta yi garambawul ga dokar bada kudaden tallafi ga masu bukata ta musamman domin kara yawan kudaden tallafin daga naira dubu bakwai zuwa naira dubu goma.
Daukar wannan mataki ya biyo bayan gabatar da rahoton kwamatin kula da al’amuran mata da cigaban al’umma na majalisar.
Da yake gabatar da rahotonsa, shugaban kwamatin kuma wakilin mazabar Birnin Kudu, Alhaji Muhammad Kabir Ibrahim, yace kwamatin ya tattauna da masu ruwa da tsaki domin duba bukatar kara yawan kudaden da ake tallafawa masu bukata ta musamman daidai da halin da rayuwa ta ke ciki a yau.
Ya ce gyaran fuskar da aka yiwa dokar ya hada da kara yawan makafi da kurame da kutare da sauran masu bukata ta musamman da ke amfana da wannan tallafi daga mutane 150 zuwa 200 a dukkan kananan hukumomin jihar 27.
Alhaji Muhammad Kabir Ibrahim ya yi nuni da cewar, karin yawan tallafin da kuma wadanda su ke amfana na daga cikin kudurin gwamnatin Malam Umar Namadi wajen inganta rayuwar masu rauni a cikin al’umma.
Ya bukaci dukkan masu bukata ta musamman a fadin jihar, su ci gaba da gudanar da addu’oi ga gwamnatin jihar da sauran shugabanni domin samun sukunin sauke nauyin da ke kan su tare da wanzuwar zaman lafiya da cigaban tattalin arziki da zamantakewa a Jigawa da Najeriya ba ki daya.
Bayan Akawun majalisar, Barrister Musa Aliyu Abubakar ya gudanar da karatu na 3 akan kudurin, sai shugaban majalisar dokokin jihar Jigawa Alhaji Haruna Aliyu Dangyatin ya sanar da amincewa da kudurin ya zamo doka.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa Majalisar Dokoki
এছাড়াও পড়ুন:
Kwara Ta Kwashe Mabarata Daga Titunan Jihar Su 94
Gwamnatin jihar Kwara ta kori mabarata 94 daga titunan Ilorin, domin tantancewa, gurfanar da su da kuma mayar da su gida.
Da take magana da ‘yan jarida yayin aikin, kwamishiniyar jin dadin jama’a da ci gaban jihar Dr Mariam Nnafatima Imam ta ce wadanda aka kama domin dawo da su sun hada da mata 43 da maza 51.
Ta ce ma’aikatar ta yi aikin dawo da mabaratan domin an haramta barace-barace a jihar Kwara.
Imam ya godewa gwamnan jihar bisa kokarin da yake yi na ganin jihar ta kawar da barace-barace a kan tituna da sauran matsalolin zamantakewa .
Kwamishinan ta ce a ko da yaushe gwamnatin jihar tana tuntubar gwamnatocin jihohin masu bara a tituna kafin a mayar da su jihohinsu.
A nasa jawabin, mataimaki na musamman ga gwamnan jihar Kwara kan sha da fataucin miyagun kwayoyi, Haliru Mikail ya ce galibin mutanen da ke bayyana kansu a matsayin mabarata suna safarar kwayoyi.
Ya ce aikin dakile barace-barace a kan tituna zai ci gaba da kasancewa domin tabbatar da zaman lafiya a tsakanin al’umma.
A nasa bangaren, shugaban sashin da ba na kariya ba, rundunar ‘yan sandan Najeriya reshen jihar Kwara Mista Adebayo Okunola ya bayyana cewa, an gudanar da aikin ne domin tsaftace jihar daga matsalolin zamantakewa yayin da wadanda aka kama tare da gurfanar da su a gaban kotun da ta dace za a hukunta su daidai da dokar jihar ta 2019.
Ya yi nuni da cewa hukumar da ke aikin za ta tabbatar da hukunta wadanda aka kama.
An gudanar da aikin ne a wasu yankuna da aka zaba a cikin birnin Ilorin da suka hada da Geri Alimi, Junction Tanke, Garage Offa, Garage Tipper da Zango, da dai sauransu.
COV/ALI MUHAMMAD RABIU