Leadership News Hausa:
2025-07-31@18:32:54 GMT

Matar Aure Ta Shiga Hannu Kan Zargin Kashe Kishiyarta A Bauchi

Published: 5th, March 2025 GMT

Matar Aure Ta Shiga Hannu Kan Zargin Kashe Kishiyarta A Bauchi

Tunin Kwamishinan ‘yansandan jihar Bauchi, CP Auwal Musa Muhammad ya umarci babban baturen ɗansanda a C Division da ya jagoranci tawaga ta musamman da za su gudanar da bincike kan lamarin a tsanake.

A cewar jami’in hulda da jama’a na rundunar, yunkurinsu a halin yanzu ya kai ga kama Fatima Mohammed, kishiya ga mamaciyar wacce a halin yanzu take tsare a hannunsu.

“Bincike na farko ya nuna cewa, akwai zargin Fatima Mohammed na da hannu a mutuwar Hajara. A yayin da ake yi mata tambayoyi, an ce ta amince ta shaƙe ta har lahira, sannan ta yi yunƙurin ɓoye laifin ta hanyar zuba mata tafasasshen ruwa tare da ƙona jikinta da buhun da ke narkewa,” in ji CSP Wakil

A sanarwar, rundunar ‘yansandan jihar Bauchi ta tabbatar da aniyarta na wanzar da adalci a kowani lokaci, inda ta ce za a mayar da kes ɗin zuwa sashin kula da manyan laifuka SCID.

Wakil ya ƙara da cewa Kwamishinan ‘yansandan jihar ya umarci tawagar kwararru da su hanzarta tattara bayanan da suka shafi wannan mutuwar ciki har da zarge-zarge da ake yi kan mutuwar Hajaran.

CP Auwal ya hori jama’an binciken da su gaggauta gudanar da bincike su tare da aiki da kwarewa inda ya tabbatar da cewa za su yi ƙoƙarin wanzar da adalci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

Gwamnatin Tarayya ta tabbatar da aniyar ta ta bunƙasa harkar kiwon dabbobi a Nijeriya a matsayin wata muhimmiyar hanya ta magance rikice-rikicen da ke tsakanin manoma da makiyaya, tare da amfani da damar tattalin arzikin da ke cikin ɓangaren.

Ɗaya daga cikin Shugabannin Kwamitin Shugaban Ƙasa kan Gyaran Harkar Kiwo, Farfesa Attahiru Jega, shi ne ya bayyana hakan a wurin taron tattaunawa tsakanin gwamnati da ‘yan ƙasa, wanda Gidauniyar Sa Ahmadu Bello ta shirya a Kaduna, a ranar Laraba.

Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya Rashin Nasarar DPP A Zagayen Farko Na Kuri’ar Kiranye Ya Nuna Rashin Amincewar Al’ummar Taiwan Da Salon Mulkin Jami’yyar

Jega ya bayyana cewa sabuwar Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo tana ɗaya daga cikin ginshiƙan da ke cikin shirin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu na sauya fasalin ɓangaren kiwon dabbobi.

Ya jaddada cewa ana aiwatar da hangen nesa na Shugaban Ƙasa ba tare da son rai na siyasa ba, tare da mayar da hankali kan haɗa kai da duk masu ruwa da tsaki, ciki har da gwamnatocin jihohi, sarakunan gargajiya, al’ummomin makiyaya da sauran muhimman masu ruwa da tsaki.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Zulum Ya Sauke Kwamishinoni Biyu Tare Da Maye Gurbinsu Da Wasu
  • ZAMFARA: APC Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Dauki Don Matsalar Tsaro Na Kara Tsananta
  • Tallafin matar Tinubu na N1bn ga ’yan gudun hijirar Binuwai ya bar baya da kura
  • NAJERIYA A YAU: Tinubu ya yi wa Arewa adalci a ayyuka da mukamai — Bayo Onanuga
  • Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega
  • Shugaban hukumar zabe ta jihar Bauchi ya rasu
  • Shugaban Hukumar Zaɓe Ta Bauchi, Ahmad Makama, Ya Rasu
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 5 a sabon hari a Alkaleri
  • Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa