Leadership News Hausa:
2025-05-01@04:47:28 GMT

Matar Aure Ta Shiga Hannu Kan Zargin Kashe Kishiyarta A Bauchi

Published: 5th, March 2025 GMT

Matar Aure Ta Shiga Hannu Kan Zargin Kashe Kishiyarta A Bauchi

Tunin Kwamishinan ‘yansandan jihar Bauchi, CP Auwal Musa Muhammad ya umarci babban baturen ɗansanda a C Division da ya jagoranci tawaga ta musamman da za su gudanar da bincike kan lamarin a tsanake.

A cewar jami’in hulda da jama’a na rundunar, yunkurinsu a halin yanzu ya kai ga kama Fatima Mohammed, kishiya ga mamaciyar wacce a halin yanzu take tsare a hannunsu.

“Bincike na farko ya nuna cewa, akwai zargin Fatima Mohammed na da hannu a mutuwar Hajara. A yayin da ake yi mata tambayoyi, an ce ta amince ta shaƙe ta har lahira, sannan ta yi yunƙurin ɓoye laifin ta hanyar zuba mata tafasasshen ruwa tare da ƙona jikinta da buhun da ke narkewa,” in ji CSP Wakil

A sanarwar, rundunar ‘yansandan jihar Bauchi ta tabbatar da aniyarta na wanzar da adalci a kowani lokaci, inda ta ce za a mayar da kes ɗin zuwa sashin kula da manyan laifuka SCID.

Wakil ya ƙara da cewa Kwamishinan ‘yansandan jihar ya umarci tawagar kwararru da su hanzarta tattara bayanan da suka shafi wannan mutuwar ciki har da zarge-zarge da ake yi kan mutuwar Hajaran.

CP Auwal ya hori jama’an binciken da su gaggauta gudanar da bincike su tare da aiki da kwarewa inda ya tabbatar da cewa za su yi ƙoƙarin wanzar da adalci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Nazarin CGTN: Ana Kara Bayyana Rashin Gamsuwa Da Sabuwar Gwamnatin Amurka Daga Ciki Da Wajen Kasar

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwastam Ta Kama Jirage Marasa Matuka Da Sauran Kayayyaki Da Darajarsu Ta Haura Naira Biliyan 921 A Legas
  • Gwamnan Sokoto Ya Amince Da Sauya Wa Manyan Sakatarori 25 Ma’aikatu A Jihar 
  • NEMA Ta Karɓi ‘Yan Nijeriya 203 Da Suka Maƙale A Libya
  • Talauci Da Rashin Ilimi Ne Ya Sa Ayyukan Boko Haram Ke Dawowa – Gwamnan Yobe
  • Nazarin CGTN: Ana Kara Bayyana Rashin Gamsuwa Da Sabuwar Gwamnatin Amurka Daga Ciki Da Wajen Kasar
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Ta yi wa saurayinta ƙaryar shekarunta 27 maimakon 47
  • Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
  • Makafi 37 Sun Zana Jarabawar JAMB A Bauchi
  • Shekara 10 ina sayar da sassan jikin ɗan Adam — Wanda ake zargi