Majalisar Kano ta yi wa dokar hukumar tace fina-finai gyaran fuska
Published: 5th, March 2025 GMT
Majalisar Dokokin Jihar Kano, ta amince da yi wa dokar da ta kafa Hukumar Tace Fina-finai ta jihar gyare-gyare.
Ɗaya daga cikin sabbi gyaran da aka yi mata shi ne na wajabta wa masu wuraren bukukuwa da taruka yin rajista da hukumar.
Abubuwa 11 da ba a sakaci da su a Ramadan — Sheikh Daurawa Kwamitin majalisa ya yi watsi da ƙorafin Natasha a kan AkpabioWannan mataki ya zo ne saboda yadda ayyukan hukumar ke jan hankali, inda sau da yawa ake samun saɓani tsakaninta da wasu.
Shugaban masu rinjaye na majalisar, Lawal Husaini Dala ne, ya bayyana cewa an yi wannan dokar gyara ne don daidaita harkokin ɗaukar fina-finai da kare addini da al’adu.
Ya ce daga yanzu ba wanda zai iya ɗaukar fim a Kano ba tare da izinin hukumar ba.
A nasa ɓangaren, Shugaban Hukumar Tace Fina-finai ta Kano, Abba El-Mustapha, ya gargaɗi masu wallafa bidiyo a shafukan sada zumunta da su guji duk wani abu da zai taɓa mutuncin addini, al’adun Hausawa, ko kuma darajar al’ummar Kano.
Ya ce hukumar za ta mara wa masu ƙirƙirar bidiyo na nishaɗi da kasuwanci, amma ba ga waɗanda ke amfani da kafafen sada zumunta don cin mutunci ba.
Haka kuma, El-Mustapha ya bayyana cewa hukumar tana da ikon ɗaukar mataki kan duk wani abu da ya saɓa wa al’adu da addini, musamman idan aka samu ƙorafi.
Yanzu haka dai majalisar dokokin jihar ta kammala nata aikin, saura gwamnan Kano ya sanya hannu a kan dokar domin ta fara aiki.
Sai dai har yanzu ba a tantance lokacin da gwamnan zai rattaɓa hannu a kai ba.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Kwamatin Tantance Ayyukan Kananan Hukumomi Na Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ya Isa Sule Tankarkar
Shugaban kwamitin kananan hukumomi na majalisar dokokin jihar Jigawa, Alhaji Aminu Zakari, ya ce kwamatin ya jinkirta rangadin kananan hukumomin jihar 27 a Zango na uku na shekarar 2024 ne a sakamakon zaben kananan hukumomi, don haka akwai bukatar ba su damar gudanar da ayyuka kafin tantance kwazon su.
Alhaji Aminu Zakari ya yi wannan tsokaci ne a sakatariyar karamar hukumar Sule Tankarkar a ci gaba da rangadin kananan hukumomi da kwamatin yake yi.
A cewar sa, kwamatin zai tantance kasafin kudin karamar hukumar na shekarar 2024 da 2025 na ayyuka ta da jerin ayyukan raya kasa, da takardun biyan kudaden ayyukan da littafin ta’ammalin kudaden na banki.
Yace kwamitin zai tantance takardun kudaden shiga tare da duba kudin tarukan bangaren zartaswa da na kansiloli domin tabbatar da bin ka’idojin kashe kudaden gwamnati.
Karamin kwamati na daya bisa jagorancin wakilin mazabar Kanya Babba Alhaji Ibrahim Hashim Kanya ya duba aikin masallacin kamsissalawati na Rugar Danqulili, da famfunan tuka tuka a Gabala/Dangwanki da Yanyawai da Fulanin Tagai da Rugar Hardo Daudu da gidan ungozoma a asibitin Jeke, da shirin noman rani a Maitsamiya.
Kazalika, kwamati na biyu bisa jagorancin wakilin mazabar Guri Alhaji Usman Abdullahi Tura Musari ya duba aikin gidan ruwa mai amfani da hasken rana a unguwar Sule Gabas da masallacin Juma’a na Hammado da makarantar Tsangaya a Danladi, da masallaci kamsissalawati na gidan mulki na Shugaban karamar hukumar da famfon tuka tuka na Gidan Idi Ruwa.
A nasa Jawabin, Shugaban karamar hukumar Sule Tankarkar Malam Tasi’u Adamu, Ya lura cewar, tantance sha’anin mulki da harkokin kudin kananan hukumomi ko shakka babu zai taimaka wajen kawo ci gaban yankunan karkara.
Malam Tasi’u Adamu ya kuma yi addu’ar samun nasarar ziyarar kwamatin domin ta yi tasiri wajen kawo cigaban rayuwar jama’ar yankin.
Usman Mohammed Zaria