Aminiya:
2025-09-17@23:28:59 GMT

Majalisar Kano ta yi wa dokar hukumar tace fina-finai gyaran fuska

Published: 5th, March 2025 GMT

Majalisar Dokokin Jihar Kano, ta amince da yi wa dokar da ta kafa Hukumar Tace Fina-finai ta jihar gyare-gyare.

Ɗaya daga cikin sabbi gyaran da aka yi mata shi ne na wajabta wa masu wuraren bukukuwa da taruka yin rajista da hukumar.

Abubuwa 11 da ba a sakaci da su a Ramadan — Sheikh Daurawa Kwamitin majalisa ya yi watsi da ƙorafin Natasha a kan Akpabio

Wannan mataki ya zo ne saboda yadda ayyukan hukumar ke jan hankali, inda sau da yawa ake samun saɓani tsakaninta da wasu.

Shugaban masu rinjaye na majalisar, Lawal Husaini Dala ne, ya bayyana cewa an yi wannan dokar gyara ne don daidaita harkokin ɗaukar fina-finai da kare addini da al’adu.

Ya ce daga yanzu ba wanda zai iya ɗaukar fim a Kano ba tare da izinin hukumar ba.

A nasa ɓangaren, Shugaban Hukumar Tace Fina-finai ta Kano, Abba El-Mustapha, ya gargaɗi masu wallafa bidiyo a shafukan sada zumunta da su guji duk wani abu da zai taɓa mutuncin addini, al’adun Hausawa, ko kuma darajar al’ummar Kano.

Ya ce hukumar za ta mara wa masu ƙirƙirar bidiyo na nishaɗi da kasuwanci, amma ba ga waɗanda ke amfani da kafafen sada zumunta don cin mutunci ba.

Haka kuma, El-Mustapha ya bayyana cewa hukumar tana da ikon ɗaukar mataki kan duk wani abu da ya saɓa wa al’adu da addini, musamman idan aka samu ƙorafi.

Yanzu haka dai majalisar dokokin jihar ta kammala nata aikin, saura gwamnan Kano ya sanya hannu a kan dokar domin ta fara aiki.

Sai dai har yanzu ba a tantance lokacin da gwamnan zai rattaɓa hannu a kai ba.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi

Hukumar NDLEA ta bayyana cewa wata ƙungiyar masu safarar miyagun ƙwayoyi ce a filin jirgin sama na Kano ta boye jakunkunan ƙwayoyi a cikin kayan matafiyan.

An kama shugaban ƙungiyar, Ali Abubakar Mohammed (wanda aka fi sani da Bello Karama), tare da wasu abokan aikinsa.

Hukumar ta ce mutanen ukun ba su da laifi kuma an zalunce su ne kawai.

An saki su ne bayan bincike da kuma ƙoƙarin diflomasiyya na tsawon makonni.

Lamarin ya tayar da hankali kan tsaro a filayen jirgin sama a Nijeriya da yadda masu aikata laifuka ke amfani da fasinjoji marasa laifi.

Hukumar ta ce za a ɗauki ƙarin matakai don hana faruwar irin wannan lamari.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
  • Karamar Hukumar Birnin Kano Ta Kaddamar Da Kula Da Lafiyar Ido Kyauta
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja