Gwamnatin Kano ta nemi Tinubu ya kori Aminu Bayero daga fadar Nassarawa
Published: 27th, February 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Kano, ta buƙaci Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ɗauki mataki na cire Sarkin Kano 15, Aminu Ado Bayero, daga Fadar Nassarawa, wanda ta ce zamansa na haddasa tashin hankali a jihar.
Mataimakin Gwamnan jihar, Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo ne, ya yi wannan kira.
Zargin Almundahana: Kotu ta ba da belin Farfesa Usman Kotu ta yanke wa matashi ɗaurin wata 6 kan satar kazaYa bayyana hakan ne lokacin da yake jawabi a Fadar Gwamnatin Kano yayin rabon kayan tallafi da ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar Tarauni, Hon.
Ya zargi wasu mutane na amfani da zaman Aminu Ado a fadar Nasarawa don cimma muradun kansu da kuma haddasa rikici a Kano.
“Muna kira ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya cire Sarkin da ya naɗa ya kuma ajiye shi a maƙabarta,” in ji Gwarzo.
“Mutanen Kano, musamman matasa, sun gaji da wannan abun kunya.
“Abun mamaki ne a ce a dimokuraɗiyya ana tura jami’an tsaro suna harba wa masu zanga-zangar lumana barkonon tsohuwa, wasu rahotanni ma suna cewa an yi amfani da harsasai na gaske.
“Da yamma, motocin sojoji sun yi sintiri a cikin gari, har ma sun tsaya a kofar gidana. Amma muna so mu bayyana cewa ba za a razana mu ba.
“Wannan dimokuraɗiyya ce, kuma dole ne a mutunta ta, ko ana so ko ba a so. Muna goyon bayan matasan da suka fito domin bayyana damuwarsu.
“Shugaban ƙasa ya ɗauke Sarkin da ya naɗa, ya kai shi jiharsa. Kano tuni tana da Sarki, kuma wannan Sarki shi ne Muhammadu Sanusi II,” in ji shi.
“A yau, ko kai waye, ko da kai ne ‘Sarkin Duniya,’ ba za ka iya naɗa Sarki a Kano ba sai dai idan kai ne Gwamna Abba Kabir Yusuf.”
Gwarzo ya jaddada cewar zaman Aminu Ado a fadar Nasarawa wata maƙarƙashiya ce don hana gwamnatin jihar gudanar da mulki yadda ya kamata.
Ya kuma soki amfani yadda jami’an tsaro ke amfani da ƙarfi a kan masu zanga-zanga, inda ya ce ‘yancin yin zanga-zangar lumana haƙƙi ne a dimokuraɗiyya.
Ya bayyana cewa mutanen Kano suna da haƙƙin neman a cire Aminu Ado Bayero, kuma ya buƙaci Shugaba Tinubu da ya ɗauki mataki cikin gaggawa domin wanzuwar zaman lafiya.
Gwamnatin Kano, ta kuma jaddada cewa doka ce ta tabbatar da naɗin tsohon sarki, kuma doka ce ta dawo da Muhammadu Sanusi II, wanda ta ce dole ne a mutunta doka kuma a bi ta yadda ya kamata.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Aminu Ado Bayero Fadar Nassarawa gwamnati Jami an Tsaro Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo mataimakin gwamna sarki
এছাড়াও পড়ুন:
Har Yanzun Ana Zaman Dar-Dar A Burkina Faso Bayan Kokarin Juyin Mulkin Da Bai SamiNasara Ba
Ana ci ga ba da zaman dar-dar a kasar Burkina faso, bayan da shugaban kasa mai ci Ibrahim traure ya sake tsallaka rijiya da baya, a wani kokarin juyin mulki wanda bai sami nasara ba a makon da ya gabata.
Shafin yanar gizo na labarai ‘Africa News’ya nakalto radiyo Faransa RFI yana fadar cewa an bankado juyin mulkin ne bayan da dukkan bakin da aka gayyata a ranar 22 ga watan Afrilu zuwa wani taro sun kasa halattan taron. Wanda ya nuna shakku kan abinda aka kulla a cikin taron.
Labarin ya kara da cewa a cikin yan kwanaki masu zuwa mutanen kasar zasu fito zanga-zanga don nuna goyon bayansu ga shugaban Traore.
Har’ila yau ana gudanar da bincike a cikin barikokin sojojin kasar a birnin Wagadugu a kokarin gano wadanda suke adawa da gwamnatin Traore, sannan suke aiki wa kasashen yamma musamman kasar Faransa wajen ganin bayan shugaba Ibrahim Traore.
Kafin haka dai an nakalto ministan tsaron kasar ta Burkina faso Muhammada Sana ya na wani bayani a tashar talabijin na kasar, kan cewa kafin su gano shirin juyin mulki sun satar maganar wayar tarho tsakanin wani babban sojan kasar da shugaban wata kungiyar ta’addaci wanda aka shirya za su kashe shugaba Traore.