Ana ci gaba da gudanar da zaɓen shugabannin ƙananan hukumomi a Jihar Katsina, inda ake fuskantar ƙarancin masu kaɗa ƙuri’a, da kuma zargin sayen ƙuri’u a wasu rumfunan zabe.

Jami’an tsaro, ciki har da ‘yansanda da NSCDC, sun sanya dokar taƙaita zirga-zirga tare da tura jami’ai wurare masu muhimmanci domin tabbatar da tsaro.

A garin Tsani, rahotanni sun nuna cewa mutum biyu kacal aka gani a rumfar zabe, yayin da aka hango motar sintiri da APC na jami’an tsaro.

Annobar Cutar Murar Tsuntsaye Ta Yadu A Jihohin Filato Da Katsina Ƴan Bindiga Sun Kai Hari A Katsina, Sun Sace Tsohon Daraktan NYSC, Janar Tsiga

A rumfar Birchi ta Kudu, inda aka yi rajistar masu zabe 808, kaɗan daga cikinsu ne suka bayyana, wasu kuma sun ce an basu ₦500 bayan sun kaɗa ƙuri’unsu. Duk da babu rahoton tashin hankali, ƙarancin fitowar masu zaɓe da zargin sayen ƙuri’u na ƙara haifar da shakku kan ingancin zaɓen.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Zaɓe

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban hukumar zabe ta jihar Bauchi ya rasu

Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta jihar Bauchi (BASIEC), Ahmed Makama Hardawa, ya rasu.

Marigayin ya rasu ne ranar Talata a Abuja, bayan ya yi fama da gajeruwar jinya.

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed ne ya tabbatar da rasuwarsa a cikin wata sanarwa ranar Laraba.

Muna tafe da karin bayani…

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Samar da makamashi mai tsafta na zamani shi ne fatanmu — Guterres
  • Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.
  • Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5
  • Manyan makarantu 2 ne kacal ke da rajista a Katsina — Gwamnati
  • Shugaban hukumar zabe ta jihar Bauchi ya rasu
  • An Kaddamar da Makon MNCH na 2025, Ya Rarraba Fakitin Bayarwa 6,000, Kayan C/S 500
  • Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa
  • Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana
  • Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati
  • ’Yan sa-kai aƙalla 100 da jami’an tsaro 30 sun mutu a bakin aiki a Katsina —Gwamnati