HausaTv:
2025-07-08@02:59:01 GMT

Kasashen Larabawa A MDD Sun Yi Watsi Da Shirin Trump Na Korar Falasdinwa Daga Gaza

Published: 15th, February 2025 GMT

Jakadun kasashen larabawa da kuma na wasu kasashen duniya sun bayyana rashin amincewarsu da shirin shugaban kasar Amurka Donal Trump na korar Falasdinawa daga yankin Zirin gaza, saun kuma bayyana hakan a matsayin wanda ya sabawa dokokin kasa da kasa.

Shirin Trump na korar Falasdinawa daga Gaza dai ya fusata kasashen duniya musamman kasashen larabawa da musulmi, sun kuma ki amincewa da duk wani abu da zai sauyawa Falasdinawa kasarsu.

Wannan yana faruwa ne bayan da HKI ta kasa kwace zirin Gazar a hannun mayakan Hamas da kawayenta na wasu kungiyoyi masu gwagwarmaya a yankin.

Amurka tana son abinda yahudawan basu same shi a yaki ba Trump ya zo ya kwace shi ya mika masu ba tare da wata wahala ba. Sun ki amincewa da hakanne don ya sabawa doka ta 49 na MDD ta shekara 1949, inji Al-Bannai wanda yake magana a madadin kasashen laraba.

Kungiyar kasashen larabawa dai sun ki amincewa da hakan sun kuma sami cikekken goyon bayan kungiyar OIC ta kasashen musulmi da kuma kungiyar yan ba ruwammu, wato ‘the Non-Aligned Movement’ (NAM).

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Elon Musk zai kafa sabuwar jam’iyyar siyasa a Amurka

Elon Musk, wanda ya taɓa zama mashawarcin Shugaban Amurka Donald Trump, ya ce zai kafa sabuwar jam’iyyar siyasa mai suna America Party.

Ya bayyana hakan ne a shafinsa na X (Twitter), makonni bayan wata taƙaddama da ta ɓarke tsakaninsa da Shugaban Amurka.

Tinubu ya umarci sojoji su murƙushe ’yan ta’adda a faɗin Najeriya  Mutum 21 sun rasu a hatsarin mota a kan hanyar Zariya–Kano

Musk, wanda attajirin mai kuɗi sosai, ya ce jam’iyyarsa za ta kasance wata hanya ta daban daga jam’iyyu biyu da ake da su yanzu, wato Republican da Democrat.

Amma har yanzu ba a bayyana ko hukumar zaɓen Amurka ta amince da rajistar jam’iyyar ba.

Amma Musk bai bayyana wanda zai jagoranci jam’iyyar ko irin manufofinta ba.

Tun da farko Musk ya fara maganar kafa sabuwar jam’iyya ne bayan samun saɓani da Donald Trump, wanda hakan ya kai sa ga sauka daga matsayinsa a gwamnatin Trump.

Yayin wata ƙuri’ar jin ra’ayi da ya gudanar a X, mutane miliyan ɗaya ne suka kaɗa ƙuri’a, kuma kashi 60 daga cikinsu sun amince a kafa sabuwar jam’iyyar siyasa a Amurka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Reuters: Amurka Tana Da Shirin Korar Falasdinawa Daga Gaza
  • China Ta Mayar Da Martani Kan Barazanar Trump Na Ƙarin Haraji Ga Kasashen BRICS
  • Kasar Rasha Tana Ci Gaba Da Karya Kadarin Kasashen Turai A Yakin Da Suke Yi A Ukraine  
  • Falasdinawa Kimani 635 Amurka da HKI Suka Kashe A Cibiyoyin Karban Abinci A Gaza
  • Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin
  • Elon Musk zai kafa sabuwar jam’iyyar siyasa a Amurka
  • Sin Da Myanmar Da Thailand Za Su Fatattaki Zambar Da Ake Yi Ta Hanyoyin Sadarwar Waya
  • Al’ummar A sassan Duniya Sun Gudanar Da Zanga-Zangar Goyon Bayan Falasdinawa
  • Shugaban Kasar Iran Ya Ce Kungiyar ECO Ta Yi Tir Da Hare-Haren HKI Kan Kasarsa
  • Sheikh Na’im Kasim Yace Kare Kasa Baya Bukatar Izini Daga Wani