HausaTv:
2025-05-22@05:02:40 GMT

Kasashen Larabawa A MDD Sun Yi Watsi Da Shirin Trump Na Korar Falasdinwa Daga Gaza

Published: 15th, February 2025 GMT

Jakadun kasashen larabawa da kuma na wasu kasashen duniya sun bayyana rashin amincewarsu da shirin shugaban kasar Amurka Donal Trump na korar Falasdinawa daga yankin Zirin gaza, saun kuma bayyana hakan a matsayin wanda ya sabawa dokokin kasa da kasa.

Shirin Trump na korar Falasdinawa daga Gaza dai ya fusata kasashen duniya musamman kasashen larabawa da musulmi, sun kuma ki amincewa da duk wani abu da zai sauyawa Falasdinawa kasarsu.

Wannan yana faruwa ne bayan da HKI ta kasa kwace zirin Gazar a hannun mayakan Hamas da kawayenta na wasu kungiyoyi masu gwagwarmaya a yankin.

Amurka tana son abinda yahudawan basu same shi a yaki ba Trump ya zo ya kwace shi ya mika masu ba tare da wata wahala ba. Sun ki amincewa da hakanne don ya sabawa doka ta 49 na MDD ta shekara 1949, inji Al-Bannai wanda yake magana a madadin kasashen laraba.

Kungiyar kasashen larabawa dai sun ki amincewa da hakan sun kuma sami cikekken goyon bayan kungiyar OIC ta kasashen musulmi da kuma kungiyar yan ba ruwammu, wato ‘the Non-Aligned Movement’ (NAM).

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Wulayati Ya Ce Samun Kalamai Masu Karo Da Juna Tsakanin Trump Da Mukarrabansa Yana Zubar Da Kwarin Gwiwa

Mai ba da shawara ga jagoran juyin juya halin Musulunci ya bayyana cewa: Kalamai masu karo da juna na Trump da mataimakansa sun zubar da kwarin gwiwa ga gwamnatin Amurka

Mai bai wa Jagoran juyin juya halin Musulunci shawara ya bayyana cewa: Sabani da ake ci gaba da yi a cikin maganganu da ayyukan Trump da takwarorinsa na haifar da rashin amincewa da gaskiyar gwamnatin Amurka.

Ali Akbar Velayati mashawarcin Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran ya yi tsokaci a cikin wani sako da ya wallafa a dandalin X kan kalamai masu cin karo da juna da jami’an Amurka suka yi.

Mai bai wa Jagoran juyin juya halin Musulunci shawara ya ce ci gaba da cin karo da juna a cikin maganganu da ayyukan Trump da mukarrabansa ya haifar da rashin amincewa da gaskata gwamnatin Amurka.

Velayati ya kara da cewa: Wannan batu ba a taba ganin irinsa ba a tarihin diflomasiyya a duniya kuma yana nuni da halin da ake ciki a cikin gwamnatin Amurka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Tattauna Hanyar Zamanantar Da Kasa A Dandalin Tattaunawa Na Masanan Sin Da Afirka
  • Wulayati Ya Ce Samun Kalamai Masu Karo Da Juna Tsakanin Trump Da Mukarrabansa Yana Zubar Da Kwarin Gwiwa
  • Babban Muftin Oman Ya Yi Suka Kan Taron Kungiyar Larabawa Saboda Rashin Saboda Rashin Ba Wa Gaza Muhimmanci
  •  Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Kashe Falasdinawa ‘Yan Gudun Hijira A Lokacin Da Suke Bacci
  • Raya Kasa Na Bukatar Bin Daidaitacciyar Hanya
  • Hare-Haren Wuce Gona Da Irin Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Janyo Shahadan Falasdinawa Masu Yawa
  • Wasu Shugabannin Turai Sun Yi Barazanar Ladabtar Da Gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Kasashen duniya 22 sun bukaci Isra’ila da ta dawo da agaji gaba daya a Gaza
  • Fahimtar Hakikanin kasar Sin
  • Iran Ta Yi Watsi Da Da’awar Kungiyar Hadin Kan Kasashen Larabawa Kan Tsibiran Kasarta