HausaTv:
2025-07-31@09:59:16 GMT

 Kasar Venezuela Ta Yi Allawadai Da Kwace Mata Jirgin Sama Da Amurka Ta Yi

Published: 7th, February 2025 GMT

MA’aikatar harkokin wajen kasar Venezue ta sanar da cewa; Abinda Amurkan ta yi sata ce a tsakar ranar Allah da ta yi wa dukiyar al’ummar Venezueal, tare da cewa za ta dauki dukkanin matakan da su ka dace domin sake dawo da jirgin saman nata.”

Sanarwar ta kuma zargin ministan harkokin wajen Amurka Marco Robio da cewa shi ne ya bayar da umarnin kwace jirgin na Venezuela.

Haka nan kuma ta kara da cewa; Kiyayyar da Robio yake yi wa kasar Venezuela ce ta sa shi kwace jirgin, da hakan ya mayar da shi zama barawon jiragen,alhali a baya, ba shi da wani aiki sai cusa kiyayya da gaba.

Ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Venezuela ta bukaci ganin an dawo ma ta da jrigin samanta da gaggawa.

Amurka dai ta kwace jirgin saman kasar Venezuela ne da ya sauka a kasar Dominican, bisa zargin yana da alaka da kamfanin man fetur na kasar. Tun a 2019 ne dai Donald Trump ya rattaba hannu akan dokar haramta haramta mu’amala da kamfanin man fetur din na  kasar Venezueal (PDVSA)

Wannan dai ba shi ne karon farko da Amurkan take kwace dukiyar kasar Venezuela ba, domin a shekarar da ta gabata ma ta kwace wata matatar mai mallakin Venezuela dake cikin kasar ta Amurka.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Venezuela

এছাড়াও পড়ুন:

 Kasar Holland Ta Hana MInistocin HKI Biyu Shiga Cikin Kasarta

A jiya Litinin ne dai gwamnatin kasar Holland ta sanar da hana wa minstocin tsaron kasa Itmir Bin Gafir, da na kudi, Bitsirael Smotrich shiga cikinta.

Kasar ta Holland ta zargi wadannan mutanen biyu da cewa suna ingiza sojojin HKI da yi wa Falasdinawa kisan kiyashi da kuma fadada yawan matsugunan ‘yan sahayoniya  a yankunan da aka ce nan ne za a kafa Daular Falasdinawa.

 Haka nan kuma gwamnatin kasar ta Holland ta kira yi jakadan HKI a birnin Hauge domin gargadinsa akan yanayin da ake ciki a Gaza, da cewa babu yadda za a iya ci gaba da jurewa akansa, ko kare dalilin jefa yankin cikin wannan halin.”

Wannan matakin na kasar Holland ya zo ne gabanin wani taro da tarayyar turai za ta yi a yau Talata domin jingine aikin tare da HKI a fagen nazari da bincike na ilimi, saboda ta ki tsagaita wutar yaki a Gaza.

Tun da fari, Fira ministan  kasar Holland Dick Schoof ya wallafa a sharin X cewa;  A yayin taron da kasashen turai za su yi, Kasarsa za ta  yi  matsin lamba akan ganin an dakatar da yarjejeniyar kasuwanci da HKI, haka nan kuma kakaba takunkumai akan shigar da kayanta na kasuwanci zuwa kasuwannin turai.

Fira ministan na kasar Holland ya ce, ya fada wa shugaban HKI Ishaq Herzog wannan matakin da suke son dauka ta hanyar tarayya turai.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Mata
  • Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Lod Da Ke Jaffa Da Makami Mai Linzami
  • Gwamnatin Sakkwato Ta Sayo Manyan Tan-tan 250 Na Sama Da Naira Biliyan 22
  •  Kasar Holland Ta Hana MInistocin HKI Biyu Shiga Cikin Kasarta
  • Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa
  • Pezeshkiya: Iran A Shirye Take Don Mu’amala Amma Bazata Bar Hakkinta Ba
  • Iran Ta Ce Amurka Ce Bayan Hare-haren Da Aka Kai Zahidan
  •  Bakai’i: Iran Tana Son Ganin An Yi Taron Gaggawa Na Kungiyar Kasashen Musulmi
  • Amurka Ta Dakatar Da Bai Wa ‘Yan Kasar Nijar Bisa Shiga Cikin Kasarta