Kasar Venezuela Ta Yi Allawadai Da Kwace Mata Jirgin Sama Da Amurka Ta Yi
Published: 7th, February 2025 GMT
MA’aikatar harkokin wajen kasar Venezue ta sanar da cewa; Abinda Amurkan ta yi sata ce a tsakar ranar Allah da ta yi wa dukiyar al’ummar Venezueal, tare da cewa za ta dauki dukkanin matakan da su ka dace domin sake dawo da jirgin saman nata.”
Sanarwar ta kuma zargin ministan harkokin wajen Amurka Marco Robio da cewa shi ne ya bayar da umarnin kwace jirgin na Venezuela.
Ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Venezuela ta bukaci ganin an dawo ma ta da jrigin samanta da gaggawa.
Amurka dai ta kwace jirgin saman kasar Venezuela ne da ya sauka a kasar Dominican, bisa zargin yana da alaka da kamfanin man fetur na kasar. Tun a 2019 ne dai Donald Trump ya rattaba hannu akan dokar haramta haramta mu’amala da kamfanin man fetur din na kasar Venezueal (PDVSA)
Wannan dai ba shi ne karon farko da Amurkan take kwace dukiyar kasar Venezuela ba, domin a shekarar da ta gabata ma ta kwace wata matatar mai mallakin Venezuela dake cikin kasar ta Amurka.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Venezuela
এছাড়াও পড়ুন:
Takht Ravanji: Iran Ba Za Ta Taba Yin Tattaunawa Akan Dakatar Da Tace Sanadarin Uranium Ba
Mataimakin ministan harkokin waje mai kula da bangaren siyasa, ya bayyana cewa; Ko kadan ba a bijiro da batun dakatar da tace sanadarin uranium a Iran ba, ko kuma batun makamanta masu linzami.
Mataimakin ministan harkokin wajen na Iran ya tabbatar da cewa, wadannan abubuwan biyu wato dakatar da ci gaba da tace sanadarin uranium da kuma makamai masu linzami, jan layi ne da jamhuriyar musulunci ta Iran ba za ta bari a ketara su ba ba kuma za ta bari a bude tattaunawa akansu ba.
Kwamitin da yake kula da tsaron kasa da kuma siyasar waje a majalisar shawarar musulunci ta Iran a karkashin jagorancin dan majalisar Ibrahim Ridhazi ya yi taro a ranar Lahadin da ta gabata, inda aka gayyaci mataimakin ministan harkokin wajen domin jin ta bakinsa akan abubuwan da suke faruwa a tattaunawar da ake yi ba kai tsaye ba da Amurka.
Ridha’i ya fada wa ‘yan jarida cewa Takht Ravanji ya kammadar da rahoto akan yadda tattaunawar take gudana a tsakanin Amurka da Iran da kasar Oman take shiga Tsakani.
Haka nan kuma ya ce; Tace sanadarin Uranium a cikin gida wani jan layi ne da ba za a tsallake shi ba.