Aminiya:
2025-11-13@20:50:40 GMT

Shugaban karamar hukuma ya biya wa al’ummarsa kudin wutar lantarki a Katsina

Published: 7th, February 2025 GMT

Majalisar Karamar Hukumar Jibiya a Jihar Kastina ta biya wa al’ummarta kudin wutar lantarki a kowane wata.

Shugaban Hukumar, Alhaji Bishir Sabi’u na cewa nan gaba za a kammala aikin layin da aka ware musu na musamman na Kamfanin Wutar Lantarki ta Kasa (TCN).

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito shi yana cewa karamar hukumar ta riga ta hada garin Jibia da layi na musamman na TCN domin garin ya rika samun wutar yadda ya kamata.

Ya ce, “duk da cewa an yi gwajin wutar, amma ba a riga an kammala aikin layin na TCN ba, kuma da ya fara aiki, al’ummar garin za su fara samun wutar lantarki tsawon awa 24.”

’Yan sanda sun sa dokar hana yawon dare a Gombe NAJERIYA A YAU: Dalilin Faɗuwar Farashin Tumatur A Kasuwa Mutuwar Almajirai: Tinubu ya buƙaci a samar da matakan kare ɗalibai

Honorabul Sabi’u wanda ya samu wakilcin mataimakinsa, Alhaji Mohammed Lawal-Jibia, ya ce karamar hukumar ta kulla yarjejeniyar da Kamfanin Wutar Lantarki na Kano (KEDCO), domin biyan kudin wutar lantarki Naira miliyan biyu ga al’umma a duk wata.

Ya ce sun dauki matakin ne domin rage wa jama’a wahalar da suke fama da ita ta tsadar rayuwa, musamman lura da yadda matsalar tsaro ta addabi yankin.

Ya bayyana cewa mma duk da haka, masu sana’o’in da ke jan wutar lantarki sosai ba sa cikin masu cin gajiyar tagomashin.

Alhaji Mohammed Lawal-Jibia ya sanar da hakan ranar Alhamis a yayin karbar bakuncin shugabannin Kungiyar ’Yan Jarida ta Kasa (NUJ) a kai kai masa ziyarar aiki.

Shugaban Karamar Hukumar ya bayyana cewa an samu wannan nasara da makamancin sa aka samu a bangaren noma da ilimi da sauransu ne da sahalewar Gwamna Dikko Radda.

A cewarsa, matsalar tsaro a karamar hukumar ta ragu sosai, yana ai cewa gwamnan bai taba yin watsi da bukatar al’ummar Jibia kan sha’anin tsaro ba.

Hasalima, gwamnan ya ba da fili da za a gina gidaje 152 domin sake tsugunar da ’yan gudun hijira a karamar hukumar.

Jibia na daga cikin kananan hukumomin Jihar Katsina mafiya fama da hare-haren ’yan ta’adda, inda da wuya a yini ba tare da hari ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Lantarki karamar hukumar wutar lantarki

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Kashe Ɗan Wasan Barau FC A Katsina

DSP Aliyu ya gargaɗi jama’a da su guji yaɗa labaran ƙarya, inda ya bayyana cewa duk wanda aka samu da laifin aikata hakan za a hukunta shi.

Ya kuma roƙi mutane su dogara da sahihan bayanai daga hukumomi, tare da tabbatar da cewa rundunar ‘yansandan ƙarƙashin CP Bello Shehu tana ƙoƙarin kare rayuka da dukiyoyin jama’a a faɗin jihar.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Wasanni Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL November 9, 2025 Wasanni Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya November 9, 2025 Wasanni Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko November 8, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Faransa: An Fara Shari’ar Shugaban ‘Yan Tawayen DRC Bisa Laifuna Akan Bil’adama
  • Almayadin Ta Sami Rahoton Hukumar Makamashin Ta Duniya  ( IEA)  Aka Cewa Iran Tana Aiki Da Dukkanin Ka’idoji
  • Shugaban Karamar Hukumar Nasarawa Ya Yi Kira Ga Jama’a Su Yi Rijista Kuma Su Karɓi Katin Zaɓe
  • Majalisar Dattawa Ta Amince da Karbo Rancen Naira Tiriliyan 1.15 Domin Cike Gibin Kasafin Kudi
  • Majalisar Jihar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Kan Laifin Rashin Ɗa’a
  • Majalisar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Bisa Zargin Rashin Ɗa’a
  • Jihar Jigawa Za ta Kashe Sama da Naira Biliyan Daya Domin Inganta Ayyukan Wutar Lantarki
  • An Bayyana Ranar Karshe Ta Biyan Kudin Aikin Hajji Mai Zuwa
  • Karamar Hukumar Gwarzo Ta Kaddamar da Sabuwar Cibiyar Kiwon Lafiya
  • ‘Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Kashe Ɗan Wasan Barau FC A Katsina