Shugaban karamar hukuma ya biya wa al’ummarsa kudin wutar lantarki a Katsina
Published: 7th, February 2025 GMT
Majalisar Karamar Hukumar Jibiya a Jihar Kastina ta biya wa al’ummarta kudin wutar lantarki a kowane wata.
Shugaban Hukumar, Alhaji Bishir Sabi’u na cewa nan gaba za a kammala aikin layin da aka ware musu na musamman na Kamfanin Wutar Lantarki ta Kasa (TCN).
Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito shi yana cewa karamar hukumar ta riga ta hada garin Jibia da layi na musamman na TCN domin garin ya rika samun wutar yadda ya kamata.
Ya ce, “duk da cewa an yi gwajin wutar, amma ba a riga an kammala aikin layin na TCN ba, kuma da ya fara aiki, al’ummar garin za su fara samun wutar lantarki tsawon awa 24.”
’Yan sanda sun sa dokar hana yawon dare a Gombe NAJERIYA A YAU: Dalilin Faɗuwar Farashin Tumatur A Kasuwa Mutuwar Almajirai: Tinubu ya buƙaci a samar da matakan kare ɗalibaiHonorabul Sabi’u wanda ya samu wakilcin mataimakinsa, Alhaji Mohammed Lawal-Jibia, ya ce karamar hukumar ta kulla yarjejeniyar da Kamfanin Wutar Lantarki na Kano (KEDCO), domin biyan kudin wutar lantarki Naira miliyan biyu ga al’umma a duk wata.
Ya ce sun dauki matakin ne domin rage wa jama’a wahalar da suke fama da ita ta tsadar rayuwa, musamman lura da yadda matsalar tsaro ta addabi yankin.
Ya bayyana cewa mma duk da haka, masu sana’o’in da ke jan wutar lantarki sosai ba sa cikin masu cin gajiyar tagomashin.
Alhaji Mohammed Lawal-Jibia ya sanar da hakan ranar Alhamis a yayin karbar bakuncin shugabannin Kungiyar ’Yan Jarida ta Kasa (NUJ) a kai kai masa ziyarar aiki.
Shugaban Karamar Hukumar ya bayyana cewa an samu wannan nasara da makamancin sa aka samu a bangaren noma da ilimi da sauransu ne da sahalewar Gwamna Dikko Radda.
A cewarsa, matsalar tsaro a karamar hukumar ta ragu sosai, yana ai cewa gwamnan bai taba yin watsi da bukatar al’ummar Jibia kan sha’anin tsaro ba.
Hasalima, gwamnan ya ba da fili da za a gina gidaje 152 domin sake tsugunar da ’yan gudun hijira a karamar hukumar.
Jibia na daga cikin kananan hukumomin Jihar Katsina mafiya fama da hare-haren ’yan ta’adda, inda da wuya a yini ba tare da hari ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Lantarki karamar hukumar wutar lantarki
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya yabawa Hukumar Makarantun Kimiyya da Fasaha ta Jiha bisa ƙirƙirar Kyautar Malami Mafi Nagarta, yana mai bayyana hakan da ɗaya daga cikin manyan manufofin da za su ƙarfafa koyo da koyarwa a fadin jihar.
A cikin wata sanarwa da Babban Jami’in Yaɗa Labaran sa, Hamisu Mohammed Gumel, ya fitar, gwamnan ya bayyana cewa bikin na farko na bada lambar yabo da aka gudanar a Dutse ya dace domin girmama malamai da suka yi fice ta hanyar jajircewa da sadaukar da kai.
Ya ƙara da cewa wannan mataki zai ƙara kwarin gwiwa, ya samar da gasa mai kyau, tare da inganta darussa a makarantu.
Namadi ya jaddada cewa ingancin ilimi bai tsaya kan gina makarantu kawai ba, yana ta’allaka ne ga ingancin malamai, kayan koyarwa da kuma yanayin makarantu.
Ya bayyana cewa gwamnatinsa ta fara ɗaukar malamai tare da horas da su akai-akai domin rage cunkoson ɗalibai da malamai da kuma horar da su sabbin dabarun koyarwa.
“Wannan shiri ɗaya ne daga cikin mafi kyawu da muka gani. Idan wani ya yi kuskure, sai a hukunta shi, yayin da duk wanda ya yi fice, wajibi ne a yaba masa. Wannan shi ne yadda ake samun cigaba,” in ji gwamnan.
Ya bukaci sauran hukumomin ilimi kamar Hukumar Gudanar da Makarantun Sakandare, Hukumar Ilimin Addinin Musulunci, da Ma’aikatar Ilimin Firamare su yi koyi da wannan tsari domin ƙara ƙarfafa gwanintar malamai a dukkan matakai.
Gwamnan ya kuma sake jaddada cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da maida hankali wajen gina makarantu, horar da malamai, da walwalar su.
Ya tabbatar da cewa za a ci gaba da baiwa bangaren ilimi goyon baya don inganta sakamakon koyo a makarantu a fadin Jihar Jigawa.
Usman Muhammad Zaria