’Yan fashin teku sun sace jirgin fasinja mutum 11 sun ɓace a Ribas
Published: 7th, February 2025 GMT
Wasu da ake zargin ’yan fashi ne sun yi awon gaba da wani jirgin ruwa ɗauke da fasinjoji 20 a hanyar ruwan daga Bonny zuwa Okrika a Jihar Ribas.
Sai dai jami’ai a ƙaramar hukumar Bonny ta ce ta kuɓutar da tara daga cikin fasinjojin yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike don ceto sauran.
Jirgin Amurka ɗauke da mutum 10 ya ɓace Magungunan Jabu: ’Yan majalisa sun nemi yin hukuncin ɗaurin rai da raiShugaban Ƙaramar hukumar Bonny, Hon Anengi Barasua Claude-Wilcox ya ce, an ceto mutanen tare da haɗin gwiwar jami’an tsaro.
Claude-Wilcox a cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Boma Waribor ya fitar a ranar Juma’a, ya ce direban jirgin fasinja ya saɓa wa ƙa’idar wucewa ta kilomita 10, wanda haramtacciyar hanya ce ga direbobin kwale-kwalen fasinja.
Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Tattaunawar tsaro da shugaban ƙaramar hukumar Bonny, Anengi Barasua Claude-Wilcox ya yi, ya nuna cewa an yi fashin wani jirgin ruwa ɗauke da fasinjoji 20 da ke kan hanyarsa ta zuwa Bonny da yammacin ranar Alhamis a yankin Isaka da ke Ƙaramar Hukumar Okrika.
“Duk da haka, ya kamata a lura da cewa an gano mutane tara aka dawo da su Fatakwal ta hanyar sa hannun jami’an tsaro na gwamnati a kan lokaci, waɗanda a halin yanzu suka ƙara ƙaimi wajen ceto sauran fasinjoji 11.
“Ya kamata a lura cewa binciken farko ya nuna cewa, direban jirgin ya bijirewa ƙa’idar hanyar kuma ya wuce kilomita 10, hanyar ruwan da aka haramta ga direbobin Jirgin ruwan fasinjoji.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Fashin jirgin ruwa Fatakwal
এছাড়াও পড়ুন:
Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Ce Ba’a Rufe Kofar Diblomasiyya Ba, Matukar HKI Ta Dakatar Da Kaiwa Kasar HKI
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araghchi ya bayyaana cewa kasarsa bata rufe kofar diblomasiyya dangane da shirinta na makamashin Nukliya ba, matukar HKI zata dakatar da hare-haren da take kaiwa kasar.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto ministan yana fadar haka a yau Lahadi a taron yan jaridun da ya kira a birnin Tehran. Ya kuma kara da cewa Iran tana son ta ci gaba da shirinta na makamashin Nukliya ta zaman lafiya ta hanyar diblomasiyya idan an bata damar yin haka.
Ministan ya ce ikidar JMI ne warware dukkan matsaloli da farko ta hanyar Diblomasiyya, da kuma tattaunawa amma ba zamu taba amincewa wani ya hanamu hakkimu na mallakar makamashi nukliya ta zaman lafiya ba. Kuma mun bayyana cewa a shirye muke a gudanar da bincike a ayyukammu. Sojojin Iran sun cilla wasu sabbin hare-hare a kan HKI a yau Lahadi da rana.
Yakin da HKI ta fara a safiyar jumma’an da ta gabata, mai kuma samun goyon bayan Amurka, don tilsatawa Iran amincewa da sharuddanta na shirin Iran na makamashin nukliya ne.