Majalisar Dokokin Jihar Jigawa ta yabawa Gwamna Umar Namadi bisa amincewarsa ga manufar majalisar, ta bullo da tsarin bada tallafin sana’oi na mazabu ba tare da jinkiri ba.

Shugaban Majalisar, Alhaji Haruna Aliyu Dangyatin ya bayyana haka a lokacin da yake kaddamar da rabon tallafi wanda wakilin mazabar Kanya a majalisar dokokin jihar,Alhaji Ibrahim Hashim Kanya, ya bai wa al’ummar garin Kanya dake karamar hukumar Babura.

 

Yana mai cewar, majalisar ta bullo da tsarin bada tallafin domin mara baya ga Kudurorin Gwamna Umar Namadi guda goma sha biyu, ta fuskar bunkasa tattali da samar da ayyukan yi ga jama’a.

A jawabinsa, wakilin mazabar Kanya Alhaji Ibrahim Hashim Kanya, ya ce mutane 1,350 ne za su amfana da tallafin daga mazabu biyar.

Ya kuma yi kira ga wadanda su ka rabauta da su yi cikakken amfani da tallafin domin su zamo masu dogaro da kawunansu.

A jawabinsa na maraba, Shugaban karamar hukumar Babura, Malam Hamisu Muhammad Garu, ya bayyana kudurinsa na aiki tare da bangaren majalisa domin ciyar da yankin gaba.

Kazalika, ya yi addu’a ga Allah SWT ya albarkaci abin da aka rabawa jama’a a yankin na Kanya.

Wakilinmu ya bamu rahoton cewar, taron ya samu halartar wasu daga cikin ‘Yan majalisa da Hakimin Kanya da kwamishinan ciniki da dai sauransu.

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa Majalisar Dokoki

এছাড়াও পড়ুন:

Falasdinu: Mahmud Abbas Ya Nada Magaji Da Kuma Mataimakasa

Shugaban Palasdinu da kuma kungiyar kwatar yencin falasdinawa PLO Mahmud Abbas ya nada magajinsa da kuma wasu mataimaka.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran, ta bayyana cewa Abbas dan shekara 89 ya nada mataimakinsa ne bayan taron majalisar gudanarwa ta gwamnatinsa  a makon da ya gabata.

Labarin ya kara da cewa kasashen yamma da yankin sun dade suna takurawa Abbas kan ya nada mataimaki da kuma wasu mataimaka sabuda rawar da gwamnatinsa zata taka bayan yakin gaza.

A yau ne majalisar zartarwa ta amince da nada Hussein Al Sheikh a matsayin mataimakin shugaban majalisar da kuma mataimakin shugaban kasa a lokaci guda.

Kamfanin dillancin labarai na gwamnatin Falasdinawan WAFA, ya bayyana cewa gwamnatin Abbas ce da hakkin sa hannu a kan yarjeniyoyi da suka shafi Falasdinu, a madadin dukkan kungiyoyin Falasdinawa, banda wadanda su ka dauke da makamai suna yakar HKI, wato Hamas da kuma Jihadul Islami a Gaza.

Mr Al Sheikh, dan shekara 64 a duniya na hannun daman Abbas ne a kungiyarsa ta fatah.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Binciken Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Cin Zali Ta Hanyar Kakaba Haraji Ya Illata Kimar Amurka
  • Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta Nijeriya
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Shirya Fara Tantance ‘Yan Fansho
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Na Iran Ya Ce: Maganar ‘Yan Sahayoniyya Rudu Ne Maras Amfani
  • Gwamna Namadi Ya Nada Aisha Mujaddadi Sabuwar Shugabar Hukumar InvestJigawa
  • Shugaban Majalisar Ƙoli ta Shari’ar Musulunci a Najeriya ya rasu
  • Hajjin 2025: Jihar Kwara Ta Fara Allurar Rigakafi Ga Maniyyata
  • Hajjin 2025: Gwamna Namadi Ya Nada Sarkin Kazaure Amirul Hajj
  • Falasdinu: Mahmud Abbas Ya Nada Magaji Da Kuma Mataimakasa
  • Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci Ta Yaba Wa Gwamna Lawal Kan Matakan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara