Tinubu ya tafi Faransa daga nan zai wuce Habasha
Published: 5th, February 2025 GMT
Shugaba Bola Tinubu a wannan Larabar ya bar Nijeriya zuwa ƙasar Faransa domin kai wata ziyara ta ƙashin kai.
Daga nan kuma Shugaba Tinubu zai wuce ƙasar Habasha inda zai halarci taron gamayyar ƙungiyar ƙasashen Afirka ta AU.
NAHCON ta tsawaita wa’adin biyan kuɗin Hajjin bana Dalilin da farashin citta ya yi tashin gwauron zaboMai bai wa Tinubu shawara kan yaɗa labarai, Bayo Onanuga a shafinsa na X, ya ce Tinubu zai tafi Paris ɗin ne gabanin tafiyar da zai yi zuwa Addis Ababa, babban birnin Habasha domin taron ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU).
A lokacin taron da za a yi a birnin na Addis Ababa a farkon mako mai zuwa, Shugaba Tinubu zai gana da shugabannin ƙasashen Afirka domin taron ƙungiyar da za a gudanar daga ranar 12 zuwa 16 ga watan Fabrairun 2025.
A yayin ziyararsa a Faransa, Tinubu zai gana da takwaran aikinsa na Faransa Emmanuel Macron.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Faransa
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaba Kasar Lebanon Ya Ce Kungiyar Hizbullah Bata Da Zabi Sai Abinda Gwamnati Ta fada
Shugaban kasar Lebanon Josept Aoun ya bayyana cewa gwamnatinsa tana son ta maida makamai a kasar Lebanon karkashin ikon hukuma kadai. Aoun ya ce kungiyar Hizbullah tana iya shiga harkokin siyasa na kasar Lebanon amma makamai na gwamnatin ne kadai.
Jaridar ‘The National Ta Kasar Amurka’ ta n akalto shugaban yana fadar haka a kasar Masar a ganawarsa da tokwaransa na lasar Abdulfattah Assisi a yau Litinin.
Aoun ya kara da cewa yana bukatar taimakon kasar Masar don gano ramukan da ake boye makamai a kasa. Sannan zai yi magana da shugaba Mahmood Abbas na Falasdinawa kan yadda za’a karbe makaman da suke hannun falasdinawa a sansanoninsu na yan gudun hijira da ke Ainul Helwa kusa da garin Saida na kudancin kasar Lebanon.
Da aka tambaye shi dangane da yankunan kasar Lebanon wadanda har yanzun HKI na mamayeda su da fursinonin kasar Lebanon da ke hannun HKI, Aoun ya ce yana magana da Amurkawa, don ita kadai ce za su takurawa HKI ta fice daga kasar Lebanon ta kuma saki yan kasar wadanda suke hannun HKI.
Kafin haka dai kungiyar Hizbullah ta bayyana cewa ba zata taba rabuwa da makamakanta sai randa babu wata kasa Isra’ila a yankin.