Aminiya:
2025-06-16@01:40:40 GMT

Sarkin Jiwa a Abuja ya yi rashin mahaifiya 

Published: 5th, February 2025 GMT

Mai martaba sarkin Jiwa a yankin birnin tarayya Abuja, Alhaji Idris Musa ya yi rashin mahaifiyarsa mai suna Hajiya Ramatu Ibrahim.

Ta rasu ne a safiyar Lahadi kamar yadda sarkin malamai na masarautar malam Jibrin Yakubu Adam ya tabbatarwa Aminiya.

Hajiya Mai Babbar Ɗaki, kamar yadda ake yi mata laƙabi, ta rasu ta bar ‘ya’ya huɗu da kuma jikoko sama da 30.

Ya ce, an gudanar da janaiza tare da binneta a Babbar maƙabartar Garin Jiwa a ranar ta Lahadin.

Tinubu zai tafi Faransa daga nan ya zarce Habasha Jami’ar ABU da ke Zariya ta yi sabon shugaba

Cikin waɗanda suka halarci jana’izar akwai Sarkin Bwari Alhaji Muhammad Auwal Ijakoro, da Gomo na Kuje Alhaji Haruna Tanko Ibrahim, da Sarkin Pai Alhaji Abubakar Sani Pai, sai kuma shugabannin ƙananan hukumomin Birnin Abuja da kewaye (AMAC) da kuma takwaransa na Abaji, wato Mista Christopher Zakka Mai Kalangu da malam Abubakar Umar Abdullahi.

A yayin ziyarar ta’aziyya da ya kai ga sarkin Jiwa a ranar Litinin, Sarkin Rubochi da ke yankin Kuje a Abuja, Alhaji Muhammad Ibrahim Pada, ya bayyana marigayiyar a matsayin uwa ta gari da ta samar da kyawawan tarbiyya abin koyi ga ‘ya’yanta, inda ya yi addu’ar Allah Ya gafarta mata da kuma yi mata rahama da Aljannah.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Bwari Jiwa

এছাড়াও পড়ুন:

Darussan Hadisin Aikin Hajjin Manzon Allah S.A.W (2)

Hadisin Aikin Hajjin Annabi (SAW) ya koyar da cewa sumbantar Hajrul As’wad yayin da aka shiga Ka’aba da kuma sake sumbantarsa yayin fita sunnah ce, amma idan mutum bai samu iko ba; ya yi sumbar ta hanyar nuni da hannu.

Hadisin ya kuma nuna mutum zai je ya yi Safa da Marwa. Zai fara da Safa kamar yadda Annabi (SAW) ya yi. Mutum zai hau kan Safa har sai ya ga dutsen, da yake sun rufe shi da gilashi sai a matsa kusa da shi. Idan ya yiwu sai a kalli Ka’aba a ambaci Allah, sannan a yi addu’a. Za a maimaita haka sau uku.

Idan mutum ya iya, ya ce “Subhanallahi wal-Hamdulillah wa La’ilaha’illallahu wal-Lahu akbar. La’ilaha’illallahu wahdahu lashariyka lahu sadaka wa’adahu wa nasara abdahu wa hadamal ahzhaba wahdahu”. Idan mutum bai iya ba, ya yi ta fadin La’ilaha’illallah. Sai ya yi addu’a.

Daga nan ya gangaro zuwa Marwa, a kan hanyarsa zai ga wani wuri da aka sanya koriyar fitila (tsakiyar Safa da Marwa), ana so ya yi sassarfa a wurin. Zai rika yin sassarfar a duk lokacin da ya zo wurin har ya kammala Sa’ayi, ba kamar sassarfar Dawafi da ake yi a kewaye uku ba kawai. Idan mutum ya hau Marwa, a can ma zai yi Zikiri ya yi addu’a.

Hadisin ya nuna cewa idan mutum ya kare Sa’ayi a kan Marwa, to ya kammala Umurarsa sai kawai ya yi aski amma ga mai Tamattu’i.

Bayan ya koma gida zai cigaba da harkokinsa na halas ciki har da kwanciya da iyali wadda aka haramta masa lokacin da ya yi harama har sai zuwa ranar Tarwiyya da za a yi niyyar Hajji.

Wani darasin Hadisin kuma shi ne, duk wanda ya warware haraminsa bayan ya kammala Umura, zai sake yin niyyar Hajji tare da fita zuwa garin Mina. Haka nan shi ma wanda bai warware ba (mai Hajjin Kirani) zai fita zuwa Mina. Sannan yana daga sunna mutum ya yi sallolin farilla guda biyar a can Mina (Azahar, La’asar, Magriba, Isha’i da Subahi). Kuma mutum zai kwana a Mina (daren ranar Arfa).

Haka nan sunna ce mutum kar ya fita zuwa Arfa har sai rana ta fito, kuma kar ya shiga Arfa sai bayan rana ta yi zawali (lokacin Azahar). Idan mutum yana da kokari, bayan an shiga Arfa sai ya tafi can Masallacin Namira ya saurari huduba; a yi Sallolin Azahar da La’asar da shi lokaci daya. Bayan kammala sallolin sai ya dawo Arfa (hukumomin can sun sanya alamomin da ke nuna kan iyakokin Arfa).

Yana daga sunna Liman ya yi huduba kafin gabatar da sallolin nan (Azahar da La’asar). Wannan ita ce huduba ta biyu, ta farkon ita ce wacce Annabi (SAW) ya yi a rana ta bakwai ga Zhul-Hijja. Akwai kuma huduba ta uku da Liman yake yi ranar Sallah, sai kuma ta hudu a ranar tafiya ta farko (kwana biyu bayan sallah).

Hadisin ya kuma koyar da mu cewa bayan mutum ya dawo daga sallolin, zai dawo cikin Arfa ya tsaya a kan abin hawansa (idan yana da hali), don haka Annabi (SAW) ya yi. Idan bai samu ba, sai ya zauna ya cigaba da yin Zikiri da addu’o’i har rana ta fadi. Idan mutum ya samu hali ya je wurin da Annabi (SAW) ya tsaya, idan bai samu shi kenan, ko ina (inda aka shata) Arfa ne. Ana so a fuskanci Alkibla yayin tsayuwar ana addu’a. Babu laifi a je a ci abinci ko a dan yawata saboda gajiya duk dai a cikin kewayen Arfar.

Annabi (SAW) ya ce fiyayyen abin da ake karantawa ranar Arfa shi ne: “La’ila’ha’illallahu wahdahu lashariyka lahu lahul mulku wa lahul hamdu yuhyi wa yumiytu wa hul hayyu layamuutu biyadihil khair wa huwa ala kulli shai’in kadiyr”, guda 100.

Bayan an taso daga Arfa sai a nufi Muzdalifa cikin natsuwa ban da gaggawa. Annabi (SAW) ya rika jan akalar abar hawansa har kanta yana taba sirdi domin tafiya a hankali zuwa Muzdalifa. Hadisin ya kuma nuna mutum ya rika horon mutane da natsuwa a yayin komawa Muzdalifa. Da farko shi ya tabbatar da ya natsu, kana sai ya hori wasu da yin hakan.

Idan mutum ya isa Muzdalifa sai ya sauka a nan ya yi Sallolin Magriba da Isha’i a hade (Magriba cikakkiya, Isha’i kasru) ba kuma tare da yin nafila ba. Ana so da an kammala a samu wuri a huta kawai, kamar yadda aka ga Manzon Allah (SAW) ya yi.

Kwanan Muzdalifa na daga cikin sunna, amma an yi sauki ga marasa lafiya ko tsofaffi tukuf-tukuf ko mata masu kiba sosai da ake ji musu tausayin ba za su iya shiga jama’a ba masu yawa, duk sai su yi gaba don su yi Jifa da wuri kana su tafi Makka. Amma matukar mutum lafiyarsa kalau; kar ya yi gaggawa, ya tsaya ya kwana a nan Muzdalifa.

Hadisin ya kuma koyar da mu cewa sunna ce bayan mutum ya kwana a Muzdalifa bayan ya yi Sallar Asuba sai ya kama hanyar Minna zuwa Masallacin Mash’aril Haram ya dan jira zuwa wayewar gari sannan ya nufi wurin Jifa.

Idan mutum ya zo wurin da ake kira Badanil Muhassar sai ya dan yi sauri don a wannan wurin ne Allah ya halakar da Aburahata sa’ilin da ya zo zai rushe Ka’aba. Amma idan mutum bai san wurin ba shi kenan, dama shi wurin Jifa ya nufa.

A wannan ranar, Jifa daya za a yi na Jamratul Akaba da tsakuwa bakwai (wannan Hadisin ya nuna girman tsakuwar kamar na wake ko gyada wadda ko an samu wani ba za a ji ma sa ciwo ba). Duk lokacin da mutum ya daga hannu zai yi Jifar ya ce Allahu Akbar har ya kammala guda bakwan.

Yana daga falalar Jifar shaidan, Annabi (SAW) ya ce “duk wanda ya yi Jifa bai ji (a ransa) cewa an yafe masa zunubansa ba, to a sannan ne ma ya yi laifi.”

Daga nan idan mutum yana Hajjin Kirani ko Tamattu’i ne sai ya nufi wurin da zai yanka dabbarsa, idan ya gama ya yi aski sai ya nufi Makka don yin Dawaful Ifada.

Da zarar ya kammala Dawafin, to komai da aka haramta masa lokacin da ya yi harama ya halasta. Amma idan bai yi wannan Dawafin ba, an halasta ma sa sauran abubuwan da aka haramta wa mai Hajji, sai dai ban da kwanciya da iyali.

Bayan nan sai ya dawo Mina ya yi kwana biyu ko kwana uku. A yayin zaman na Mina kullum mutum zai yi Jifa uku. Daga nan Aikin Hajji ya kare, sai mutum ya je Makka ya yi Dawafin bankwana.

A takaice, wadannan su ne kadan daga cikin darussan Hadisin da Annabi (SAW) ya sanar da cewa duniya ta zo ta ga yadda zai yi Aikin Hajji a shekarar da ya fara yi (SAW).

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An tallafa wa mata 250 da abinci da kayan sana’a a Kaduna
  • Dalilin da muka soke tattaunawar nukiliya da Amurka — Iran
  • Wakilin Sin: Matakin Amurka Game Da Harajin Kwastam Bai Yi La’akari Da Rarar Cinikayyar Hidimomi Ba
  • Gwamnan Kaduna ya bai wa sabon Sarkin Moro’a sandar mulki
  • Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata
  • Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • Hajjin 2025: Yadda Alhazan Nijeriya 7 Suka Rasa Rayukansu A Saudi Arabiya
  • Darussan Hadisin Aikin Hajjin Manzon Allah S.A.W (2)
  • NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya