Aminiya:
2025-11-03@02:15:26 GMT

Sarkin Jiwa a Abuja ya yi rashin mahaifiya 

Published: 5th, February 2025 GMT

Mai martaba sarkin Jiwa a yankin birnin tarayya Abuja, Alhaji Idris Musa ya yi rashin mahaifiyarsa mai suna Hajiya Ramatu Ibrahim.

Ta rasu ne a safiyar Lahadi kamar yadda sarkin malamai na masarautar malam Jibrin Yakubu Adam ya tabbatarwa Aminiya.

Hajiya Mai Babbar Ɗaki, kamar yadda ake yi mata laƙabi, ta rasu ta bar ‘ya’ya huɗu da kuma jikoko sama da 30.

Ya ce, an gudanar da janaiza tare da binneta a Babbar maƙabartar Garin Jiwa a ranar ta Lahadin.

Tinubu zai tafi Faransa daga nan ya zarce Habasha Jami’ar ABU da ke Zariya ta yi sabon shugaba

Cikin waɗanda suka halarci jana’izar akwai Sarkin Bwari Alhaji Muhammad Auwal Ijakoro, da Gomo na Kuje Alhaji Haruna Tanko Ibrahim, da Sarkin Pai Alhaji Abubakar Sani Pai, sai kuma shugabannin ƙananan hukumomin Birnin Abuja da kewaye (AMAC) da kuma takwaransa na Abaji, wato Mista Christopher Zakka Mai Kalangu da malam Abubakar Umar Abdullahi.

A yayin ziyarar ta’aziyya da ya kai ga sarkin Jiwa a ranar Litinin, Sarkin Rubochi da ke yankin Kuje a Abuja, Alhaji Muhammad Ibrahim Pada, ya bayyana marigayiyar a matsayin uwa ta gari da ta samar da kyawawan tarbiyya abin koyi ga ‘ya’yanta, inda ya yi addu’ar Allah Ya gafarta mata da kuma yi mata rahama da Aljannah.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Bwari Jiwa

এছাড়াও পড়ুন:

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazanar Sa Ga Nijeriya

Kwankwaso ya kuma buƙaci gwamnatin Tarayya da ta ƙarfafa hulɗar diflomasiyya da Amurka ta hanyar naɗa jakadu na musamman da kuma jakadun dindindin domin kare muradun Nijeriya a matakin ƙasa da ƙasa.

Ya kamata gwamnatin Nijeriya ta naɗa jakadu na musamman da kuma jakadun dindindin domin wakiltar muradunmu yadda ya kamata a kasashen waje,” in ji shi.

A ƙarshe, yayi kira ga ƴan Nijeriya da su zauna cikin haɗin kai da juriya, yana mai cewa lokaci ne da ya kamata a fifita zumunci fiye da rarrabuwar kai.

Yan uwa ƴan Nijeriya, lokaci ne da muke buƙatar haɗin kai fiye da komai. Allah ya taimaki Nijeriya,” in ji Kwankwaso.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba November 2, 2025 Manyan Labarai Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba November 2, 2025 Manyan Labarai 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su November 2, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazanar Sa Ga Nijeriya
  • Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara
  • Wadi Al-Salam: Maƙabartar Musulmai Mafi Girma A Duniya
  • Maganin Nankarwa (3)
  • Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya 
  • Rikicin PDP: Tsagin Wike ya dakatar da Damagum
  • Dan Majalisar Jema’a/Sanga, Daniel Amos, Ya Koma Jam’iyyar APC
  • Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC
  • Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta