Aminiya:
2025-09-18@02:38:09 GMT

Sarkin Jiwa a Abuja ya yi rashin mahaifiya 

Published: 5th, February 2025 GMT

Mai martaba sarkin Jiwa a yankin birnin tarayya Abuja, Alhaji Idris Musa ya yi rashin mahaifiyarsa mai suna Hajiya Ramatu Ibrahim.

Ta rasu ne a safiyar Lahadi kamar yadda sarkin malamai na masarautar malam Jibrin Yakubu Adam ya tabbatarwa Aminiya.

Hajiya Mai Babbar Ɗaki, kamar yadda ake yi mata laƙabi, ta rasu ta bar ‘ya’ya huɗu da kuma jikoko sama da 30.

Ya ce, an gudanar da janaiza tare da binneta a Babbar maƙabartar Garin Jiwa a ranar ta Lahadin.

Tinubu zai tafi Faransa daga nan ya zarce Habasha Jami’ar ABU da ke Zariya ta yi sabon shugaba

Cikin waɗanda suka halarci jana’izar akwai Sarkin Bwari Alhaji Muhammad Auwal Ijakoro, da Gomo na Kuje Alhaji Haruna Tanko Ibrahim, da Sarkin Pai Alhaji Abubakar Sani Pai, sai kuma shugabannin ƙananan hukumomin Birnin Abuja da kewaye (AMAC) da kuma takwaransa na Abaji, wato Mista Christopher Zakka Mai Kalangu da malam Abubakar Umar Abdullahi.

A yayin ziyarar ta’aziyya da ya kai ga sarkin Jiwa a ranar Litinin, Sarkin Rubochi da ke yankin Kuje a Abuja, Alhaji Muhammad Ibrahim Pada, ya bayyana marigayiyar a matsayin uwa ta gari da ta samar da kyawawan tarbiyya abin koyi ga ‘ya’yanta, inda ya yi addu’ar Allah Ya gafarta mata da kuma yi mata rahama da Aljannah.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Bwari Jiwa

এছাড়াও পড়ুন:

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
  • Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
  • Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
  • Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
  • Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja