An yi kiyasin adadin tafiye-tafiyen fasinjoji tsakanin yankuna zai kai biliyan 4.8 a duk fadin kasar Sin daga ranar 14 ga watan Janairu zuwa ta 2 ga watan Febrairu, wato rabin farko na kwanaki 40 na zirga-zirgar bikin bazara. 

Adadin ya nuna karuwar kashi 7.2 cikin dari bisa makamancin lokaci na bara, a cewar tawagar aiki ta musamman da aka kafa don saukake ayyukan da suka shafi zirga-zirgar bikin bazara, wanda aka fi sani da chunyun.

Hukumar FCTA Ta Rufe Asibitin Da Ke Aiki Ba Bisa Ka’ida Ba A Kuje Abinda Ya Kamata Ku Sani Dangane Da Wasan Athletico Madrid Da Getafe

Zirga-zirgar fasinjoji ya karu tun daga ranar 30 ga watan Janairu, inda adadin tafiye-tafiyen ya zarce miliyan 300 a ranakun 31 ga watan Janairu da ta 1 ga watan Fabrairu, duk sun zarce na bara, a cewar wata cibiyar bincike da ci gaba karkashin ma’aikatar sufuri, tana mai cewa ana sa ran hakan na iya ci gaba da faruwa a lokacin hutun.

Har ila yau, a ranar 2 ga Fabrairu kadai, an yi kiyasin adadin tafiye-tafiye zai kai miliyan 319.32, tare da manyan tituna da ke da kaso mafi girma na tafiye-tafiye miliyan 301.02, a cewar tawagar aiki ta musamman. (Mai fassara: Mohammed Yahaya)

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Namadi Ya Biya Sama Da Naira Biliyan Daya Ga Tsofaffin Ma’aikata

Hukumar Tsarin Fansho na Hadin Gwiwa tsakanin Jiha da Kananan Hukumomi a Jihar Jigawa ta bayyana cewa ta raba sama da Naira Biliyan 1 da dubu 500 ga tsofaffin ma’aikata 569.

Yayin da yake jawabi ga wadanda suka ci gajiyar shirin a gaban Gidan Fansho kafin fara rabon kudin, Shugaban Ma’aikatan Gwamnatin Jihar, Alhaji Muhammad K. Dagaceri, ya bayyana tsarin fansho na jihar a matsayin daya daga cikin mafi nagarta a kasar nan.

A cewarsa, fiye da jihohi ashirin sun kai ziyara jihar Jigawa domin koyon yadda take tafiyar da shirin fansho.

Ya jinjina wa Gwamna Umar Namadi saboda dagewarsa da kuma jajircewarsa wajen dorewa da inganta tsarin fansho a jihar.

Alhaji Dagaceri ya yabawa Gwamna Namadi kan goyon bayansa da matakan da ya dauka tun bayan hawansa mulki domin inganta tsarin, yana mai jaddada irin tasirin alherin da shirin ke yi ga tsofaffin ma’aikata da daukacin ma’aikatan gwamnati.

Ya bukaci tsofaffin ma’aikata da wadanda ke aiki yanzu da su ci gaba da yi wa gwamnati addu’a, tare da nuna godiya ga Gwamna Namadi bisa irin ayyukan alherinsa.

A nasa jawabin, Shugaban hukumar ta Fansho, Dr. Binyaminu Shitu Aminu, ya bayyana cewa fiye da naira biliyan 1 da rabi ne za a raba tsakanin tsofaffin ma’aikata 569.

“Wannan adadi ya kunshi nau’o’in biyan kudi daban-daban, ciki har da hakkokin ritaya, hakkokin mutuwa da sauran ragowar hakkokin fansho na mamatan ma’aikata,” In ji Dr. Aminu.

Dr. Aminu ya kara da cewa, cikin wadanda za su amfana, 287 sun fito ne daga ma’aikatan jiha, 158 daga kananan hukumomi, yayin da 124 suka fito daga Hukumar Ilimin Kananan Hukumomi (LEA).

Ya kara da cewa, za a biya sama da Naira Miliyan 875 ga ma’aikatan da suka yi aiki a karkashin gwamnatin jiha, sannan sama da Naira Miliyan 355 kuma ga wadanda suka fito daga kananan hukumomi, da kuma sama da naira miliyan 274 ga wadanda suka fito daga LEA.

Shugaban hukumar ya tabbatar da cewa hukumar za ta ci gaba da biyan hakkokin fansho a kan kari, ciki har da biyan fansho na wata wata a cikin mako na farko na kowane wata.

 

Ya jaddada kudurin gwamnatin jihar na inganta walwalar ma’aikata, domin samun rayuwa mai kyau da kwanciyar hankali bayan kammala aikin.

Usman Muhammad Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rashin Nasarar DPP A Zagayen Farko Na Kuri’ar Kiranye Ya Nuna Rashin Amincewar Al’ummar Taiwan Da Salon Mulkin Jami’yyar
  • Shugaban hukumar zabe ta jihar Bauchi ya rasu
  • Adadin Falasdinawan da Isra’ila take kashewa a Gaza yanzu ya haura 60,000
  • Kwamitin Neman Sabuwar Karamar Hukumar Kanya Babba Ya Gabatar Da Takardar Bukatarsa Ga Majalisar Dattawa
  • Shugaban Ivory Coast Ouattara zai sake takara wa’adi na huɗu
  • Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana
  • Remi Tinubu ta bai wa waɗanda harin Benuwe ya shafa tallafin Naira biliyan ɗaya
  • Remi Tinubu ta ba da tallafin Naira biliyan ɗaya ga waɗanda harin Benuwe ya shafa
  • Gwamna Namadi Ya Biya Sama Da Naira Biliyan Daya Ga Tsofaffin Ma’aikata
  • Sin Ta Samar Da Manyan Manhajojin AI Sama Da 1500