Sanata mai wakiltar Kano ta Kudu a Majalisar Dattawa, Abdurrahman Kawu Sumaila ya tabbatar da ficewarsa daga jam’iyyar NNPP zuwa APC.
Sumaila ya tabbatar wa Aminiya ficewarsa a wani saƙon kar ta kwana, bayan wallafa wa a shafinsa na Facebook.
Majalisun jihohi sun buƙaci a kawo ƙarshen matsalar tsaro Gwamna da jiga-jigan siyasa a Delta sun fice daga PDP zuwa APC“Gaskiya ne na koma APC.
Sanatan ya jaddada cewa matakin da ya ɗauka na sauya sheƙar ya yi shi ne domin inganta rayuwar al’ummar mazaɓarsa, da kuma tabbatar da ci gabansu mai dorewa.
Kawu dai ya daɗe da raba gari da tafiyar Kwankwasiyya da NNPP da ya yi takara ƙarƙashin ta, wanda ya sanya wasu da dama suka daɗe da hasashen zai sauya sheƙa zuwa tsohuwar jam’iyyarsa ta APC da ya bari a wancan lokacin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kawu Sumaila Kwankwasiyya Kwankwaso
এছাড়াও পড়ুন:
An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a Australia
Rundunar ’yan sandan ƙasar Australia ta kama wata ’yar asalin Najeriya da ke ƙasar Australia, Binta Abubakar bisa zarginta da safarar ɗalibai daga ƙasar Papua New Guinea tare da tilasta musu yin aikin da ba a biya a gonaki a faɗin jihar Ƙueensland da sunan bayar da tallafin karatu.
Binta mai shekara 56, an kama ta ne a ranar Laraba a filin jirgin saman Brisbane a lokacin da ta isa ƙasar Papua New Guinea, inda take zaune.
Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawar mutum bayan kwanaki 8 Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — FayemiKamen nata ya biyo bayan wani bincike na tsawon shekaru biyu da ƙungiyar masu fataucin bil-Adama ta AFP ta yankin Arewa, wacce ta ƙaddamar da bincike kan ayyukanta a watan Yulin 2022 bayan samun bayanai daga ’yan sandan Ƙueensland.
A cewar AFP, “Wani gungun ‘yan asalin Papua New Guinea (PNG) da suka yi ƙaura zuwa Australia don yin karatu, an yi zargin cewa an tilasta musu yin aiki ba tare da son ransu ba a gonaki.”
An ba da rahoton cewa matar mai izinin zama ƙasashen biyu ta yaudari aƙalla ƴan ƙasar PNG 15, masu shekaru tsakanin 19 zuwa 35, zuwa Australia tsakanin Maris 2021 da Yuli 2023 ta hanyar kamfaninta, BIN Educational Serɓices and Consulting, da kuma ta hanyar ba da guraben karatu na bogi.
Rahoton ya bayyana cewa, shafin intanet na kamfaninta ya yi iƙirarin bayar da “daidaitaccen tsarin zamani don ilimi, horarwa da kuma aikin yi.”
Sai dai ’yan sandan sun ce gaskiyar lamarin ya sha bamban sosai.
Da zarar sun isa Australia, an yi zargin cewa an tilasta wa ɗaliban su sanya hannu kan jerin takaddun doka da ke tilasta su su biya kuɗin da ke da alaƙa da karatun, kuɗin jirgi, aikace-aikacen samar da biza, inshora da kuma kuɗaɗen doka.”