’Yan bindiga sun sace makiyaya 5, da shanu 1,200 a Kaduna
Published: 17th, April 2025 GMT
Mazauna gundumar Kufana a Ƙaramar Hukumar Kajuru ta Jihar Kaduna sun shiga cikin fargaba sakamakon jerin hare-haren ’yan bindiga da ya yi sanadiyyar sace mutane biyar da kuma kwashe shanu 1,200 cikin kwanaki hudu.
Babban Jami’in Gundumar, Mista Stephen Maikori, ya tabbatar da faruwar hare-haren a ranar Laraba.
A cewarsa, lamari na farko ya faru ne a daren Talata, 8 ga Afrilu, 2025, lokacin da ’yan bindiga suka kai hari kauyen Mashigi Boka-Libere, wani matsugunin Fulani, da misalin karfe 10 na dare.
Maikori ya ce maharan sun kwashe garken shanu guda 12, inda kowanne garke yake da kimanin shanu 100, wanda ya kai jimillar dabbobi 1,200.
Dangote: Har yanzu gidajen mai ba su rage farashin mai ba Najeriya da gwamnatin sojin Nijar sun sasantaYa ce maharan sun wuce ta kauyen Dogon Noma, inda suka kai hari ga mazauna suka kuma sace babura biyu daga hannun Mista Abednego Samuel da Mista Danjuma John.
A ranar Litinin, 7 ga Afrilu, da misalin karfe 6 na safe, an sace mutane uku daga Ungwan Kaje Afogo.
Maikori ya ce wani harin kuma ya faru a daren Alhamis, 10 ga Afrilu, a al’ummar Afogo Gari, inda aka sace Miss Patience Audi da Mista Arewa Anthony.
Ya ce, “Muna ci gaba da tuntubar jami’an tsaro da iyalai da abin ya shafa.”
Kokarin da aka yi na tuntubar kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, DSP Mansir Hassan, bai yi nasara ba saboda yana cikin taro kuma bai amsa kiran waya ba a lokacin da ake tattara wannan rahoto.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: hare hare
এছাড়াও পড়ুন:
‘ADC za ta mayar da APC jam’iyyar adawa a 2027’
Tsohon Ministan Sufuri, Idris Umar, ya bayyana cewa jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ce za ta ceto Najeriya daga halin da take ciki, tare da mayar da APC jam’iyyar adawa a Zaɓen 2027.
Yayin wani taron haɗin gwiwar jam’iyyu na adawa a Gombe, an amince da amfani da ADC a matsayin dandalin siyasa na bai ɗaya domin fuskantar zaɓen 2027.
Gwamnatin Tinubu na shirya mana zagon ƙasa — ADC NAJERIYA A YAU: Sarƙaƙiyar da ke gaban Haɗakar ADC: Atiku ko Peter ObiTaron ya gudana a Shugleez Event Centre wanda ya samu halartar fitattun ‘yan adawa daga sassa daban-daban na jihar.
Idris ya ce za su yi haɗakar ce ba wai kawai don karɓar mulki ba, sai dai domin ceton ƙasa da talakawa daga matsin tattalin arziƙi da rashin shugabanci nagari.
Shugaban ADC na jihar, Auwal Abba Barde, ya ce jam’iyyar na samun karɓuwa daga sabbin mambobi tare da tabbatar musu da wakilci
Aminiya ta ruwaito cewa an kafa kwamitin rajistar sabbin mambobi ƙarƙashin tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe, John Lazarus Yoriyo, da AVM Adamu Fura a matsayin mataimaki.
Tsohon shugaban matasan APC, Sunusi Abdullahi Ataka, ya ce haɗakar za ta yi tasiri wajen karɓar mulki a Gombe da Najeriya gaba ɗaya.
Wasu daga cikin mahalarta sun haɗa da wakilin Farfesa Isa Ali Pantami, Abubakar Abubakar BD, da sauran jiga-jigai na jam’iyyar ADC.
Bayanai sun ce a yanzu haka jam’iyyar ADC da ’yan haɗaka da wasu jagororin ’yan hamayya suka dunƙule a ƙarƙashin inuwarta ta fara karɓe tsarin jagorancin jam’iyyar PDP a jihohin Yobe da Adamawa da kuma Gombe.
Sun ce an samu ’yan PDP da dama da suka sauya sheƙa zuwa ADC, ciki har da waɗanda suka riƙe manyan muƙamai a baya.
A Jihar Adamawa wasu daga cikin ƙusoshin jam’iyyar da suka riƙe mukamai a matakai daban daban na jiha tuni suka sauya sheƙa zuwa jam’iyyar ’yan hadaka ta ADC inda kawo yanzu shugabannin jami’yyar PDP a ƙananan hukumomi goma a cikin jihar suka fice daga cikin jam’iyyar.