Aminiya:
2025-07-09@05:15:27 GMT

’Yan bindiga sun sace makiyaya 5, da shanu 1,200 a Kaduna

Published: 17th, April 2025 GMT

Mazauna gundumar Kufana a Ƙaramar Hukumar Kajuru ta Jihar Kaduna sun shiga cikin fargaba sakamakon jerin hare-haren ’yan bindiga da ya yi sanadiyyar sace mutane biyar da kuma kwashe shanu 1,200 cikin kwanaki hudu.

Babban Jami’in Gundumar, Mista Stephen Maikori, ya tabbatar da faruwar hare-haren a ranar Laraba.

A cewarsa, lamari na farko ya faru ne a daren Talata, 8 ga Afrilu, 2025, lokacin da ’yan bindiga suka kai hari kauyen Mashigi Boka-Libere, wani matsugunin Fulani, da misalin karfe 10 na dare.

Maikori ya ce maharan sun kwashe garken shanu guda 12, inda kowanne garke yake da kimanin shanu 100, wanda ya kai jimillar dabbobi 1,200.

Dangote: Har yanzu gidajen mai ba su rage farashin mai ba Najeriya da gwamnatin sojin Nijar sun sasanta

Ya ce maharan sun wuce ta kauyen Dogon Noma, inda suka kai hari ga mazauna suka kuma sace babura biyu daga hannun Mista Abednego Samuel da Mista Danjuma John.

A ranar Litinin, 7 ga Afrilu, da misalin karfe 6 na safe, an sace mutane uku daga Ungwan Kaje Afogo.

Maikori ya ce wani harin kuma ya faru a daren Alhamis, 10 ga Afrilu, a al’ummar Afogo Gari, inda aka sace Miss Patience Audi da Mista Arewa Anthony.

Ya ce, “Muna ci gaba da tuntubar jami’an tsaro da iyalai da abin ya shafa.”

Kokarin da aka yi na tuntubar kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, DSP Mansir Hassan, bai yi nasara ba saboda yana cikin taro kuma bai amsa kiran waya ba a lokacin da ake tattara wannan rahoto.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hare hare

এছাড়াও পড়ুন:

Miliyoyin Yan Najeriya Ne Suka Gudanar da Tattakin Ashoora Wasu Kuma A Makarantunsu…

Miliyoyin yan Najeriya ne suka gudanar da tattakin Ashoora a birne daban daban a kasar a jiya Lahadi.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran, da farko ya nakalto daruwan da suka fito tattakin na Ashoora a Abuja babban birnin kasar a safiyar jiya Lahadi.

A wannan karon dai masu tattakin Ashoora a Abuja sun fito ba tare da sanya bakaken kaya ba saboda kaucewa rikici da kuma kamu daga Jami’an tsaro a birnin, kamar yadda suka sabayi a shekarun da suka gabata.

Labarin ya kara da cewa an gudanar da irin wannan tattakin na Ashoora a garurwa kimai 25 a duk fadin kasar, kuma an kammala ba tare da wata matsala ba.

An gudanar da tattaki a jihar Bauchi da kuma Jihar Yobe, wasu masu makokin Ashoora sun gudanar da su ne a cikin makarantu ko kuma masallatansu ko kuma wasu wurare da da suka kebe don haka Kungiyar muassasar Rasulul Azam sun gudanar da taron a makaransu da ke dan bare a birnin kano da kuma wasu wurare.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An ceto mutum 6 daga hannun masu garkuwa a Kebbi
  • TCN Ta Wayar Da Kan Al’ummomin Kaduna Kan Illar Lalata Kayan Wuta Da Gini Karkashen Babbar Wayar Wuta 
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka ‘Yan Sa-kai Sama Da 70 A Filato
  • Gwamna Peter Mbah Ya Ƙaddamar Da Jiragen Kasuwanci 3 Na ‘Enugu Air’ Mallakin Jihar
  • Sojoji Sun Fatattaki Ƴan Bindigar Da Suka Zo Sace Wani Ɗan China
  • Adadin Mutanen Da Suka Mutu A Ambaliyar Texas Ya Haura 80
  • Miliyoyin Yan Najeriya Ne Suka Gudanar da Tattakin Ashoora Wasu Kuma A Makarantunsu…
  • Turji: Sai ka sako mutanen da ka sace za a yi sulhu — Gwamnatin Sakkwato
  • Za A Fara Sufurin Ma’aikata Da Ɗaliban Kaduna Kyauta A Bas
  • Gwamna ya gargaɗi sarakuna kan mamaye filayen kiwo a Gombe