Hukumar Alhazai Ta Jihar Neja Ta Fara Rabon Unifom da Jakunkunan Hannu Ga Maniyya
Published: 16th, April 2025 GMT
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Neja ta kaddamar da rabon sutura da jakunkunan hannu masu nauyin kilo 8 ga maniyyatan bana, a matsayin wani ɓangare na shirye-shiryen aikin Hajji na shekarar 2025.
A lokacin da yake jawabi yayin kaddamar da rabon, Shugaban Hukumar, Sheikh Muhammad Awwal Aliyu, ya bayyana cewa rabon kayayyakin na da matuƙar muhimmanci wajen tabbatar da sauƙin tafiya da kuma aikin Hajji ba tare da wata tangarda ba ga maniyyatan jihar.
Shugaban wanda Daraktan Gudanarwa, Babani Aliyu Yahaya, ya wakilta a yayin bayar da kayan ga Jami’in Alhazai na Ƙaramar Hukumar Chanchaga, ya ce kayayyakin na maniyyatan da suka kammala biyan kuɗin kujerunsu ne.
Daraktan Gudanarwar ya kuma yi kira ga waɗanda har yanzu ba su kammala biyan kuɗinsu ba da su gaggauta, tare da buƙatar waɗanda ke da niyyar zuwa Hajji da su hanzarta biya domin gudanar da aikin cikin tsari.
A nasa jawabin bayan karɓar kayayyakin, shugaban karamar hukumar Chanchaga, Alhaji Abu Sufyanu ya yi alkawarin raba kayan yadda ya dace, tare da tabbatar da cewa za su gudanar da ayyukansu bisa nagarta da gaskiya.
Daga Aliyu Lawal
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Jigawa Ta Amince da Sama da Naira Biliyan 2.6 Domin Aikin Hajjin 2026
Daga Usman Muhammad Zaria
Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da naira biliyan 2.6 domin gudanar da ayyukan Hajjin shekarar 2026.
Kwamishinan Yada Labarai, Matasa, Wasanni da Al’adu na jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed ne ya bayyana hakan jim kadan bayan kammala taron Majalisar Zartarwa ta Jiha da aka gudanar a gidan gwamnati da ke Dutse, babban birnin jihar.
A cewarsa, majalisar ta amince da kashe sama da naira biliyan 2 da miliyan 651 domin ayyukan Hajjin 2026, biyo bayan gabatar da bukatar da Sakataren Gwamnatin Jihar (SSG) ya yi.
Alhaji Sagir Musa Ahmed ya ce za a yi amfani da kudaden ne a bangarorin sufuri da jijigilaAlhazai, jin dadinsu, ayyukan lafiya da kuma shirye-shiryen gudanarwa.
Sauran bangarorin sun hada da duk wasu muhimman abubuwa da za su tabbatar da ingantaccen tsari da nasarar aikin Hajji ga Alhazan jihar Jigawa.
Kwamishinan ya kara da cewa, majalisar ta kuma amince da kashe sama da Naira Biliyan 1 da Miliyan 300 domin tallafin karatu (bursary) ga dalibai 19,716 da aka tantance kwanan nan.
Ya bayyana cewa daga cikin adadin, akwai dalibai maza 12,638, da mata 7,088 da ke karatu a manyan makarantu 77.
Ya ce wannan tallafi zai taimaka wajen bunkasa harkar ilimi, rage nauyin kudi a kan iyaye da iyalai, tare da karfafa gwiwar dalibai su yi fice a karatunsu.