Hukumar Alhazai Ta Jihar Neja Ta Fara Rabon Unifom da Jakunkunan Hannu Ga Maniyya
Published: 16th, April 2025 GMT
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Neja ta kaddamar da rabon sutura da jakunkunan hannu masu nauyin kilo 8 ga maniyyatan bana, a matsayin wani ɓangare na shirye-shiryen aikin Hajji na shekarar 2025.
A lokacin da yake jawabi yayin kaddamar da rabon, Shugaban Hukumar, Sheikh Muhammad Awwal Aliyu, ya bayyana cewa rabon kayayyakin na da matuƙar muhimmanci wajen tabbatar da sauƙin tafiya da kuma aikin Hajji ba tare da wata tangarda ba ga maniyyatan jihar.
Shugaban wanda Daraktan Gudanarwa, Babani Aliyu Yahaya, ya wakilta a yayin bayar da kayan ga Jami’in Alhazai na Ƙaramar Hukumar Chanchaga, ya ce kayayyakin na maniyyatan da suka kammala biyan kuɗin kujerunsu ne.
Daraktan Gudanarwar ya kuma yi kira ga waɗanda har yanzu ba su kammala biyan kuɗinsu ba da su gaggauta, tare da buƙatar waɗanda ke da niyyar zuwa Hajji da su hanzarta biya domin gudanar da aikin cikin tsari.
A nasa jawabin bayan karɓar kayayyakin, shugaban karamar hukumar Chanchaga, Alhaji Abu Sufyanu ya yi alkawarin raba kayan yadda ya dace, tare da tabbatar da cewa za su gudanar da ayyukansu bisa nagarta da gaskiya.
Daga Aliyu Lawal
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
‘Mutum 600 da suka bace a ambaliyar Mokwa sun mutu’
’Yan Majalisar Wakilai daga jihohin Neja da Kwara sun shaida wa majalisar cewa mutum 600 da suka bace a ambaliyar garin Mokwa kuma har yanzu ba a gan su ba, za a dauka su ma sun mutu.
Dan majalisa Joshua Audu Gana (Neja) da Saba Ahmed Umaru (Kwara) ne suka bayyana hakan a yayin gabatar da wani kudurin gaggawa a zauren majalisar a ranar Laraba.
Sun ce mummunar ambaliyar da aka yi a ranakun 28 da 29 ga watan Mayun da ya gabata sanadin mamakon ruwan saman da aka tafka ta yi barna sosai a karamar hukumar ta Mokwa a jihar Neja, sannan ta tsallaka har karamar hukumar Edu ta jihar Kwara.
Lakurawa sun kashe mutum 15 a harin ramuwar gayya a Sakkwato NAJERIYA A YAU: Ɓoyayyun Ƙalubalen Da Sabuwar Haɗakar ADC Za Ta Iya FuskantaA cewar ’yan majalisar, yayin da aka tabbatar da mutuwar mutum 500, su kuma ragowar sama da 600 da aka ce sun bace kuma har yanzu babu labarin su, su ma za a kirga su a cikin matattun, la’akari da munin ambaliyar.
’Yan majalisar sun kuma ce ambaliyar ta lalata gidaje sama da 4,000, ta jikkata sama da mutum 200, sannan ta shanye gonaki da gine-gine, ta kuma raba dubban mutane da muhallansu.
Daga nan ne majalisar ta yi shiru na minti daya don girmama wadanda ambaliyar ta shafa, sannan ta yaba wa Shugaban Kasa Bola Tinubu saboda amincewa a bayar da tallafin Naira biliyan biyu ga wadanda lamarin ya shafa.
Majalisar, bayan tafka muhawara, ta kuma amince da kudurin sannan ta ba da umarnin inganta matakan dakile ambaliya a yankin da ma sauran yankunan da ke cikin barazanar ambaliyar, cikin gaggawa.
Kazalika, majalisar ta kuma umarci Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Kasa (NEMA) da ta samar da kayayyakin agaji da na tsafta ga al’ummomin da lamarin ya shafa domin kaucewa sake barkewar cututtuka.