Aminiya:
2025-12-10@20:09:18 GMT

Kotu ta tsare ’yan TikTok 2 a Kano

Published: 14th, April 2025 GMT

Wata Kotun Majistire mai lamba 7 a Kano, ta bayar da umarnin tsare wasu ’yan TikTok biyu kan zargin wallafa wasu bidiyon batsa a shafukansu na dandalin sada zumunta.

Hukumar Tace Fina-Finai ta Kano ce ta gurfanar da ababen zargin biyu — Isa Kabir Brigade da Fatima Adam Kurna — kan wallafa bidiyon da suka saɓa wa tarbiyya da addini.

An rantsar da shugabannin ƙananan hukumomi 34 na Katsina ’Yar shekara 66 ta haifi ɗanta na 10 da kanta

Sai dai bayan lauyan da ke ɓangaren masu shigar da ƙara, Garzali Maigari Bichi ya karanta musu ƙunshin tuhume-tuhumen, sun musanta wasu daga ciki.

Dangane da hakan ne Alƙalin Kotun, Halima Wali ta bayar da umarnin tsare ababen zargin tare da ɗage zaman kotun zuwa ranar 24 ga watan Afrilu.

Ana iya tuna cewa dai Hukumar Tace Fina-Finai ta Kano ta ɗaura ɗamarar tsaftace dandalan sada zumunta ta hanyar kame da ladabtar da masu wallafe-wallafen duk wani abu da ya ci karo da tarbiyya da addini.

Ko a bayan nan sai da hukumar ta gurfanar da wasu mutum biyu — waɗanda aka yankewa hukuncin ɗauri na shekara guda ko zaɓin biyan tara ta Naira dubu 100 — kan wallafa bidiyon batsa a shafukansu na TikTok.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Rikicin Iyakar Thailand da Cambodia Ya Tilasta wa Dubban Mutane Barin Muhallansu

Jami’ai sun ce mutane sama da dubu 500 ne kawo yanzu aka tursasawa barin muhallansu a Thailand da kuma Cambodia a yayin da rikicin kan iyaka tsakanin ƙasashen biyu ke ƙara ƙamari.

Rundunar sojin Thailand ta ce Cambodia ta harba mata dubban makaman roka tun bayan da suka soma rikici da juna.

Dubban mutane ne suke guduwa domin tserewa lugudan makaman roka da ake harbawa daga Cambodia.

Kazalika Thailand ma na ci gaba da kai wa Cambodia hare-hare ta sama.

Shugaba Donald Trump na Amurka ya ce yana kyautata tsammanin zai gana da  shugabannin kasashen biyu ta wayar tarho, wanda ya matsa musu lamba aka cimma kwarya-kwaryar yarjejeniyar tsagaita wuta a watan Yulin da ya gabata.

To sai dai ministan harkokin wajen Thailand ya gargadi Amurka akan amfani da wata barazana ko haraji domin tursasa komawa teburin sulhu don cimma yarjejeniyar zaman lafiya.

bbc

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • EFCC ta tsare Malami kan binciken kuɗaɗen Abacha
  • Zanga-zanga ta ɓarke kan zargin sojoji da kashe mata a Adamawa
  • Rikicin Iyakar Thailand da Cambodia Ya Tilasta wa Dubban Mutane Barin Muhallansu
  • An kama wani mutum a Abuja yana ƙoƙarin kai harsasai ga ’yan bindiga a Zamfara
  • ’Yan jaridar Daily Trust da Trust TV sun lashe kyautar binciken ƙwaƙwaf ta Wole Soyinka ta bana
  • Saudiya da Qatar Zasu Gina Layin Dogo Mai Sauri Tsakanin Kasashen Biyu
  •  Kasashen Iran Da Turkiya Za Su Bunkasa Alakarsu A Fagen Ilimi Da Musayar Fasaha
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Abincin Da Mutane Ke Ci Ke Zamewa Guba
  • IRGC: Makaman Iran Sun Fada Kan Matatan Man Haifa Har Sau Biyu A Yakin Kwanaki 12
  • Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima Ya Isa Abidjan Wajen Rantsar da Shugaba Ouattara