Wata Kotun Majistire mai lamba 7 a Kano, ta bayar da umarnin tsare wasu ’yan TikTok biyu kan zargin wallafa wasu bidiyon batsa a shafukansu na dandalin sada zumunta.
Hukumar Tace Fina-Finai ta Kano ce ta gurfanar da ababen zargin biyu — Isa Kabir Brigade da Fatima Adam Kurna — kan wallafa bidiyon da suka saɓa wa tarbiyya da addini.
Sai dai bayan lauyan da ke ɓangaren masu shigar da ƙara, Garzali Maigari Bichi ya karanta musu ƙunshin tuhume-tuhumen, sun musanta wasu daga ciki.
Dangane da hakan ne Alƙalin Kotun, Halima Wali ta bayar da umarnin tsare ababen zargin tare da ɗage zaman kotun zuwa ranar 24 ga watan Afrilu.
Ana iya tuna cewa dai Hukumar Tace Fina-Finai ta Kano ta ɗaura ɗamarar tsaftace dandalan sada zumunta ta hanyar kame da ladabtar da masu wallafe-wallafen duk wani abu da ya ci karo da tarbiyya da addini.
Ko a bayan nan sai da hukumar ta gurfanar da wasu mutum biyu — waɗanda aka yankewa hukuncin ɗauri na shekara guda ko zaɓin biyan tara ta Naira dubu 100 — kan wallafa bidiyon batsa a shafukansu na TikTok.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Zaɓen 2027 ya hana ni korar wasu ma’aikata – Bago
Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umaru Bago, ya jaddada goyon bayansa ga wa’adin mulki ɗaya kacal ga gwamnonin, yana mai cewa hakan zai inganta aiki da kuma inganta harkokin mulki.
Ya bayyana hakan ne a lokacin da yake rantsar da sababbin zaɓaɓɓun shugabannin Ƙananan hukumomi, mataimakan shugabannin, Kwamishinoni da shugabannin hukumar a ɗakin taro na Hauwa Isah Wali da ke gidan gwamnati, Minna babban birnin jihar.
Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 2, sun ƙwato makamai a Borno Osimhen ya lashe kyautar gwarzon ɗan wasan bana na TurkiyyaBago ya bayyana cewa, saboda zaɓen 2027 ne ya hana shi ya ɗauki tsauraran matakai kan wasu jami’an idan ba don zaben da ke tafe ba, yana mai cewa tsarin wa’adi ɗaya ne zai bai wa shugabanni damar yin taka-tsantsan ba tare da matsin lamba na siyasa ba.
“Ni mai goyon bayan wa’adi ɗaya ne ga gwamnoni domin abin takaicin mun dawo kan batutuwan siyasa, komai na Najeriya cike yake da siyasa, abin takaici ne!
“Akwai abubuwan da zan iya yi a yau, amma zan yi magana ne a kai bayan zaɓe. Dole ne in sallami wasu ma’aikata da ba su da amfani, amma ba zan iya ba saboda zaɓe, sun faɗi jarabawarsu da yawa, ba za a iya yi musu ƙarin girma ba, amma nauyi ne a kan tsarin. Idan da zango ɗaya ne ake yi, da na fi yanke hukunci fiye da wanda nake a yau,” in ji shi.