Za A Samar Da Ababen Hawa Ga Malaman Sakandare A Jigawa
Published: 12th, April 2025 GMT
Gwamnatin jihar Jigawa ta ce za ta samar da ababen hawa ga shugabannin makarantun babbar sakandare a fadin jihar.
Kwamishinan ilimi na jihar, Farfesa Isa Yusuf Chamo, ne ya bayyana hakan yayin wani taro da ya gudanar da shugabannin makarantu a garin Dutse.
A cewarsa, za a gyara gidajen ma’aikatan makarantun sakandare domin saukaka matsalar masauki ga malamai da sauran ma’aikata da ba malamai ba.
Farfesa Chamo, wanda Mataimaki na Musamman ga Gwamna kan Harkokin Ilimi, Malam Abdullahi Hudu, ya wakilta, ya ce taron ya na da nufin tattauna shirin dawowa makarantu bayan hutun da aka yi a jihar.
Ya bayyana cewa, gwamnatin jihar ta sanya bangaren ilimi a sahun gaba saboda muhimmancinsa ga ci gaban jihar.
Kwamishinan ya nuna cewa gwamnatin jihar ta dauki malamai 7,000 domin inganta tsarin koyarwa a makarantu, inda ya kara da cewa za a dauki ma’aikatan girki na J-Cook domin kara karfafa harkar gudanarwar makarantu.
A jawabansu daban-daban, wasu daga cikin Daraktoci da Shugabannin makarantu, sun bukaci a sake duba kudaden gudanar da makarantu, da samar da kwamfutoci da kayan aikinsu, da bayar da tallafi da kuma samar da malamai domin inganta ayyukan koyarwa.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Tankin ruwa ya kashe mutum 4, wasu sun jikkata a Jigawa
An shiga jimami a garin Zugai da ke Ƙaramar Hukumar Roni ta Jihar Jigawa, bayan da wani tankin ruwa ya faɗo tare yin sanadin rasuwar mutum da jikkata wasu.
Daga cikin waɗanda suka rasu har da wata mace mai juna biyu.
An yanke wa shugaban ISWAP hukuncin ɗaurin shekara 20 a gidan yari Gwamna Abba ya gabatar da N1.36trn a matsayin kasafin 2026Majiyoyi sun bayyana cewa lamarin ya auku ne kwana uku bayan shugaban Ƙaramar Hukumar, ya raba ruwa ga masu sana’r sayar da ruwa, lamarin da ya haifar da ce-ce-ku-ce a tsakanin wasu mutane.
Tankin ruwa, wanda ke amfani da hasken rana wajen samar da ruwa, ya fashe yayin da mutane da yawa suka taru a ƙasa domin ɗibar ruwa.
Shaidu sun ce tankin ya rushe ba zato ba tsammani, inda mutum uku suka mutu nan take, waɗanda suka jikkata aka garzaya da su asibiti.
Shugaban Majalisar Ƙaramar Hukumar Roni, Dokta Abba Ya’u Roni, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya tabbatar da mutuwar mutum huɗu.
Dokta Abba, ya ce fashewar tankin ta faru ne sakamakon iska mai ƙarfi wadda ta turo tankin ya faɗo kan mutane.
Ya ƙara da cewa: “Na umarci mataimakina da jami’an majalisa su kai ziyara ƙauyen don tabbatar da cewa duk waɗanda suka ji rauni an kula da su.”