Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-12-06@22:49:59 GMT

Za A Samar Da Ababen Hawa Ga Malaman Sakandare A Jigawa

Published: 12th, April 2025 GMT

Za A Samar Da Ababen Hawa Ga Malaman Sakandare A Jigawa

Gwamnatin jihar Jigawa ta ce za ta samar da ababen hawa ga shugabannin makarantun babbar  sakandare a fadin jihar.

Kwamishinan ilimi na jihar, Farfesa Isa Yusuf Chamo, ne ya bayyana hakan yayin wani taro da ya gudanar da shugabannin makarantu a garin Dutse.

A cewarsa, za a gyara gidajen ma’aikatan makarantun sakandare domin saukaka matsalar masauki ga malamai da sauran ma’aikata da ba malamai ba.

Farfesa Chamo, wanda Mataimaki na Musamman ga Gwamna kan Harkokin Ilimi, Malam Abdullahi Hudu, ya wakilta, ya ce taron ya na da nufin tattauna shirin dawowa  makarantu bayan hutun da aka yi a jihar.

Ya bayyana cewa, gwamnatin jihar ta sanya bangaren ilimi a sahun gaba saboda muhimmancinsa ga ci gaban jihar.

Kwamishinan ya nuna cewa gwamnatin jihar ta dauki malamai 7,000 domin inganta tsarin koyarwa a makarantu, inda ya kara da cewa za a dauki ma’aikatan girki na J-Cook domin kara karfafa harkar gudanarwar makarantu.

A jawabansu daban-daban, wasu daga cikin Daraktoci da Shugabannin makarantu, sun bukaci a sake duba kudaden gudanar da makarantu, da samar da kwamfutoci da kayan aikinsu, da bayar da tallafi da kuma samar da malamai domin inganta ayyukan koyarwa.

 

Usman Muhammad Zaria 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Shettima Ya Taya Sarkin Gumel Murna Tare da Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Bunkasa Bangaren Noma

Daga Usman Muhammad Zaria

Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima, ya yaba da gagarumin cigaba a harkar noma da Gwamna Umar Namadi ya samar cikin shekaru biyu kacal na mulkinsa.

Ya bayyana haka ne a masarautar Gumel cikin Jihar Jigawa, yayin kaddamar da sabon masallacin Juma’a da Gidauniyar Kashim Shettima ta gina a matsayin wani ɓangare na bikin zagayowar cikar Sarkin Gumel shekaru 45 a kan karaga.

A cewarsa, abin sha’awa ne yadda Gwamna Umar Namadi ya mayar da harkar noma a jihar Jigawa zuwa ta zamani cikin shekaru biyu kacal.

Ya jinjina wa Gwamnan da al’ummar Jihar Jigawa bisa wannan ci gaba mai armashi.

Kashim Shettima ya kara taya Sarkin Gumel, Alhaji Muhammadu Sani, murnar cika shekaru 45 a matsayin Sarkin Gumel, tare da yi masa fatan alkhairi.

Ya tabbatar da ci gaba da jajircewar Gidauniyar Kashim Shettima wajen inganta rayuwar ‘yan Najeriya.

A jawabinsa, Mai Alfarma Sarkin Musulmi Muhammadu Sa’ad Abubakar, ya yaba wa Mataimakin Shugaban Kasa bisa kaddamar dadMasallacin.

Ya kuma taya Sarkin Gumel murnar cika shekaru 45 a kan karaga, tare da yi masa fatan alheri.

Shi ma a nasa jawabin, Gwamna Umar Namadi ya jinjina wa Mataimakin Shugaban Kasa bisa gina Masallacin Juma’ar.

Namadi ya kuma yaba da jinjinar da VP ya yi kan sauyin da aka samu a harkar noma ta Jigawa, yana mai alkawarin cewa za a cigaba da kara himma a bangaren noma da ma dukkan ababen da za su ciyar da jihar gaba.

Gwamnan ya kara jinjina wa Mai Alfarma Sarkin Musulmi  da sauran manyan baki bisa halartar taro.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ma’aikatar Ayyuka da Sufuri ta Jigawa Ta Bada Kiyasin Kasafin Kudi na Sama da Naira Biliyan 161
  • Ma’aikatar Shari’a ta Jihar Jigawa ta Kare Kasafin Kudin 2026 a Gaban Majalisa
  • Mutum 3 sun mutum yayin haƙar rijiya a Kano
  • Yaƙin M23 Ya ci Gaba a Congo Duk da Sulhu da Rwanda
  • Putin Na Rasha Ya Ce; Kasarsa Da India Za Su Kara Girman Kasuwancinsu
  • Shettima Ya Taya Sarkin Gumel Murna Tare da Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Bunkasa Bangaren Noma
  • Na kashe N100bn a kan harkar tsaro a 2025 — Zulum
  • DSS ta kama likitan da ke duba ’yan bindiga a dazukan Kwara
  • Fadlallah Na Hizbullah Ya Yi Kiran Hadin Kai A Tsakanin Musulmi Da Larabawa Domin Fuskantar Kalubale
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar da Wutar Lantarki a Yankunan Kananan Hukumomin Jihar