Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-24@22:08:06 GMT

Za A Samar Da Ababen Hawa Ga Malaman Sakandare A Jigawa

Published: 12th, April 2025 GMT

Za A Samar Da Ababen Hawa Ga Malaman Sakandare A Jigawa

Gwamnatin jihar Jigawa ta ce za ta samar da ababen hawa ga shugabannin makarantun babbar  sakandare a fadin jihar.

Kwamishinan ilimi na jihar, Farfesa Isa Yusuf Chamo, ne ya bayyana hakan yayin wani taro da ya gudanar da shugabannin makarantu a garin Dutse.

A cewarsa, za a gyara gidajen ma’aikatan makarantun sakandare domin saukaka matsalar masauki ga malamai da sauran ma’aikata da ba malamai ba.

Farfesa Chamo, wanda Mataimaki na Musamman ga Gwamna kan Harkokin Ilimi, Malam Abdullahi Hudu, ya wakilta, ya ce taron ya na da nufin tattauna shirin dawowa  makarantu bayan hutun da aka yi a jihar.

Ya bayyana cewa, gwamnatin jihar ta sanya bangaren ilimi a sahun gaba saboda muhimmancinsa ga ci gaban jihar.

Kwamishinan ya nuna cewa gwamnatin jihar ta dauki malamai 7,000 domin inganta tsarin koyarwa a makarantu, inda ya kara da cewa za a dauki ma’aikatan girki na J-Cook domin kara karfafa harkar gudanarwar makarantu.

A jawabansu daban-daban, wasu daga cikin Daraktoci da Shugabannin makarantu, sun bukaci a sake duba kudaden gudanar da makarantu, da samar da kwamfutoci da kayan aikinsu, da bayar da tallafi da kuma samar da malamai domin inganta ayyukan koyarwa.

 

Usman Muhammad Zaria 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya dakatar da ’yan sanda daga tsaron manyan mutane a Najeriya

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya bai wa ’yan sanda umarnin daina tsaron manyan mutane a faɗin Najeriya.

Mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga ne, ya bayyana hakan a ranar Lahadi.

’Yan sanda sun ƙaryata jita-jitar kai wa coci hari a Gombe ’Yan bindiga sun kashe ’yan sanda 5 a Bauchi

Onanuga, ya ce daga yanzu ’yan sanda za su mayar da hankalinsu ne aikin kare al’umma da yaƙar ’yan ta’adda.

An ɗauki wannan mataki ne a wani taron tsaro da aka gudanar a Abuja, wanda manyan shugabannin tsaro suka halarta, ciki har da shugabannin ’yan sanda, sojin sama, sojin ƙasa da hukumar DSS.

Sabon tsarin ya nuna cewa duk wani babban mutum da yake buƙatar tsaro dole ne, ya nemi jami’an tsaro daga Hukumar NSCDC maimakon ’yan sanda.

Najeriya ba ta da isassun ’yan sanda a yankunan karkara, kuma hakan yana haifar da tsaiko wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

Saboda haka Shugaba Tinubu, ya umarci a ƙara yawan ’yan sandan da ke bai wa jama’a tsaro.

Onanuga, ya kuma ce Shugaban Ƙasa ya amince da ɗaukar ƙarin sabbin ’yan sanda 30,000.

Gwamnatin Tarayya za ta haɗa kai da gwamnatocin jihohi domin inganta cibiyoyin horas da ’yan sanda a faɗin Najeriya.

Taron tsaron da aka gudanar a ranar Lahadi, ya samu halartar Babban Hafsan Sojin Ƙasa, Laftanar Janar Waidi Shaibu, Babban Hafsan Sojin Sama, Air Marshal Sunday Kelvin Aneke, Sufeto Janar na ’Yan Sanda, Kayode Egbetokun, da Darakta-Janar na DSS, Tosin Adeola Ajayi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An rufe duk makarantu a Jihar Bauchi saboda matsalar tsaro
  • An rufe duk makarantu a Jihar Bauchi na saboda matsalar tsaro
  • NAJERIYA A YAU: Halin Da Shirin Samar Da Tsaro A Makarantun Najeriya Ke Ciki
  • Tinubu ya dakatar da ’yan sanda daga tsaron manyan mutane a Najeriya
  • Gwamnatin Kebbi Ta Bayar da Umarnin Rufe Makarantu a Jihar
  • An gano wurin da ’yan bindiga ke tsare da ɗalibai 25 da aka sace a Kebbi
  • Gwamnatin Katsina Ta Umurci a Gaggauta Rufe Dukkan Makarantun Jihar
  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Za Ta Mayar Da Rarar Kudi Ga Maniyyatan 2026
  • Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Ba da Umarnin Rufe Makarantu 41 Nan Take
  • Ɗalibai 215 da malamai 12 aka sace a Makaranta a Neja — CAN