Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-12-01@20:38:29 GMT

Za A Samar Da Ababen Hawa Ga Malaman Sakandare A Jigawa

Published: 12th, April 2025 GMT

Za A Samar Da Ababen Hawa Ga Malaman Sakandare A Jigawa

Gwamnatin jihar Jigawa ta ce za ta samar da ababen hawa ga shugabannin makarantun babbar  sakandare a fadin jihar.

Kwamishinan ilimi na jihar, Farfesa Isa Yusuf Chamo, ne ya bayyana hakan yayin wani taro da ya gudanar da shugabannin makarantu a garin Dutse.

A cewarsa, za a gyara gidajen ma’aikatan makarantun sakandare domin saukaka matsalar masauki ga malamai da sauran ma’aikata da ba malamai ba.

Farfesa Chamo, wanda Mataimaki na Musamman ga Gwamna kan Harkokin Ilimi, Malam Abdullahi Hudu, ya wakilta, ya ce taron ya na da nufin tattauna shirin dawowa  makarantu bayan hutun da aka yi a jihar.

Ya bayyana cewa, gwamnatin jihar ta sanya bangaren ilimi a sahun gaba saboda muhimmancinsa ga ci gaban jihar.

Kwamishinan ya nuna cewa gwamnatin jihar ta dauki malamai 7,000 domin inganta tsarin koyarwa a makarantu, inda ya kara da cewa za a dauki ma’aikatan girki na J-Cook domin kara karfafa harkar gudanarwar makarantu.

A jawabansu daban-daban, wasu daga cikin Daraktoci da Shugabannin makarantu, sun bukaci a sake duba kudaden gudanar da makarantu, da samar da kwamfutoci da kayan aikinsu, da bayar da tallafi da kuma samar da malamai domin inganta ayyukan koyarwa.

 

Usman Muhammad Zaria 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Barau ya musanta zargin gwamnatin Kano, ya soki gwamna Abba

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin, ya buƙaci Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, da ya daina siyasantar da harkar tsaro a jihar.

Ya ce kamata ya yi gwamnan ya mayar da hankali kan matsalolin da ke damun jihar.

Yadda ’yan mata ke kuɗancewa da kasuwancin fara a Kano DSS ta gayyaci Datti Baba-Ahmed kan zargin kalaman tayar da hankali

Barau, ya yi wannan bayani ne bayan gwamnatin Kano ta zarge shi da yin magana inda ya nemi gwamnatin ta mayar da hankali kan tsaro.

Ya ce matsalolin tsaro a ƙasar nan, ciki har da hare-haren ’yan bindiga a wasu yankunan Kano, suna buƙatar haɗin kai daga kowa.

A cikin wata sanarwa daga mai taimaka masa, Ismail Mudashiru, ya fitar, Barau ya ce zargin gwamnatin ba gaskiya ba ne.

Ya ƙalubalanci gwamnatin ta nuna bidiyon da ya yi maganar da za ta iya haddasa matsalar tsaro.

Ya ce wannan zargi ƙarya ne kuma na da nufin ɓata masa suna.

Ya ƙara da cewa bai taɓa yin wata magana da za ta kawo tangarɗa ga harkar tsaro ba.

A maimakon haka, ya ce yana aiki tare da sauran jami’ai domin inganta tsaro a Kano da sauran sassan Najeriya.

Barau, wanda shi ne Mataimakin Kakakin ECOWAS, ya buƙaci Gwamna Abba da ya “farka daga bacci” ya jagoranci jihar yadda ya kamata.

Ya ce a baya Kano na gogayya da Legas wajen ci gaba, amma rashin kyakkyawan shugabanci ya janyo mata koma baya.

Ya ce ya bai wa rundunonin ’yan sanda motocin aiki, ya bai wa jami’an ’yan sanda babura a Kano ta Arewa, sannan ya gyara wasu sassan hedikwatar ’yan sanda ta Kano.

Haka kuma, ya gina ofisoshin ’yan sanda a wurare daban-daban, ya tallafa wa hukumar DSS, sannan ya taimaka wajen kafa makarantu na horar da jami’an NSCDC, Hukumar Ayyukan ’Yan Sanda, da Hukumar Shige da Fice a wasu yankunan Kano.

Ya ce ya sanya fitilu masu amfani da hasken rana a yankinsa domin taimaka wa zirga-zirga da daddare.

A cewarsa, waɗannan ayyukan suna nuna irin gudunmawar da yake bayarwa wajen inganta tsaro, don haka ya kamata gwamnatin jihar ta yi koyi da shi maimakon ɓata masa suna.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Najeriya Ta Kara Ƙaimi Wajen Kawar da Cutar HIV Nan da 2030
  • Gwamnatin Kano Ta Kara Jaddada Dokar Haramcin Yin Haya da Babur a Jihar
  • Jihar Jigawa Ta Mayar da Rarar Kudi Sama da Naira Miliyan 50 Ga Maniyyatan Aikin Hajjin 2026
  • Mutum 6 sun jikkata a rikici manoma da makiyaya a Jigawa
  • ’Yan bindiga sun kashe tsohuwa, sun sace mutum 3 a Kano
  • Yadda aka horar da mata 100 sana’o’in dogaro da kai a Gombe
  • Barau ya musanta zargin gwamnatin Kano, ya soki gwamna Abba
  • Lebanon ta shigar da kara ga Kwamitin Tsaro bayan Isra’ila ta Gina katanga a Yankinta
  • Ziyarar Da Larijani Ya Kai Pakistan Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Kara Dankon Zumunci
  • Sarakuna sun goyi bayan Gwamnatin Gombe kan yaƙi da cin zarafin mata