Za A Samar Da Ababen Hawa Ga Malaman Sakandare A Jigawa
Published: 12th, April 2025 GMT
Gwamnatin jihar Jigawa ta ce za ta samar da ababen hawa ga shugabannin makarantun babbar sakandare a fadin jihar.
Kwamishinan ilimi na jihar, Farfesa Isa Yusuf Chamo, ne ya bayyana hakan yayin wani taro da ya gudanar da shugabannin makarantu a garin Dutse.
A cewarsa, za a gyara gidajen ma’aikatan makarantun sakandare domin saukaka matsalar masauki ga malamai da sauran ma’aikata da ba malamai ba.
Farfesa Chamo, wanda Mataimaki na Musamman ga Gwamna kan Harkokin Ilimi, Malam Abdullahi Hudu, ya wakilta, ya ce taron ya na da nufin tattauna shirin dawowa makarantu bayan hutun da aka yi a jihar.
Ya bayyana cewa, gwamnatin jihar ta sanya bangaren ilimi a sahun gaba saboda muhimmancinsa ga ci gaban jihar.
Kwamishinan ya nuna cewa gwamnatin jihar ta dauki malamai 7,000 domin inganta tsarin koyarwa a makarantu, inda ya kara da cewa za a dauki ma’aikatan girki na J-Cook domin kara karfafa harkar gudanarwar makarantu.
A jawabansu daban-daban, wasu daga cikin Daraktoci da Shugabannin makarantu, sun bukaci a sake duba kudaden gudanar da makarantu, da samar da kwamfutoci da kayan aikinsu, da bayar da tallafi da kuma samar da malamai domin inganta ayyukan koyarwa.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
BUA ya tallafa wa ɗaliban Sakkwato 200 da miliyan 40
Kamfanin samar da siminti na BUA ya bayar da tallafin karatu Naira miliyan 40 ga ɗalibai 200 da ke manyan makarantu a jihohin tsohuwar Jihar Sakkwato.
An bayar da tallafin domin ganin sun cimma burinsu a fannin ilmi.
An kai hari gidan jami’in ɗan sanda a Yobe Ɗaliban Jami’ar Unijos 8 sun mutu a hatsarin motaƊaliban da suka ci gajiyar sun haɗa da matasa 50 daga Sakkwato, 50 daga Kebbi da 50 daga Zamfara, sai 50 a Wamakko inda cibiyar kamfanin simintin yake.
Kowane ɗalibi zai karɓi Naira dubu 200, an samu ninkin ɗaliban kuɗin ma an samu ƙari da kashi 100 bisa ga shekarun baya.
Shugaba kuma Daraktan kamfanin, Injiniya Yusuf Binji ya ce sun ninka yawan ɗalibai daga 100 zuwa 200 haka kuɗin daga dubu 100 zuwa 200.
Injiniya Binji ya bayyana tallafin karatun matsayin saka jari ne da zai samar da al’ummar mai ɗorawa a gaba.
Ya yi kira ga waɗanda suka ci gajiyar su yi abin da ya dace kuma kamfani zai bibiyi karatunsu.
Shugaban Kamfanin na BUA ya gode wa gwamnatin jiha kan samar musu filin kasuwanci ba tsangwama.
Mai baiwa Gwamanan Sakkwato shawara, Honarabul Usman Arzika Fako ya ce tallafin zai bunƙasa ilmi da samar da aikin yi ga matasa.
Ya yaba wa kamfanin ga wannan hoɓɓasar, akwai buƙatar a duba wasu ɓangarori suma a yi abin da ya kamata.
Balkisu Bello Muhammad, ɗaliba daga Kebbi ta bayyana BUA ginshiƙi ne na samar da cigaba ta gode wa kamfanin kan wannan saka jarin da suka yi da za su ci gajiyarsa a gaba.
Umar Bello ɗalibi daga Zamfara ya nuna farin cikinsa ga kamfanin yadda ya ɗaga karatunsa zai samu nasara a gaba.