Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-08-16@11:58:17 GMT

Za A Samar Da Ababen Hawa Ga Malaman Sakandare A Jigawa

Published: 12th, April 2025 GMT

Za A Samar Da Ababen Hawa Ga Malaman Sakandare A Jigawa

Gwamnatin jihar Jigawa ta ce za ta samar da ababen hawa ga shugabannin makarantun babbar  sakandare a fadin jihar.

Kwamishinan ilimi na jihar, Farfesa Isa Yusuf Chamo, ne ya bayyana hakan yayin wani taro da ya gudanar da shugabannin makarantu a garin Dutse.

A cewarsa, za a gyara gidajen ma’aikatan makarantun sakandare domin saukaka matsalar masauki ga malamai da sauran ma’aikata da ba malamai ba.

Farfesa Chamo, wanda Mataimaki na Musamman ga Gwamna kan Harkokin Ilimi, Malam Abdullahi Hudu, ya wakilta, ya ce taron ya na da nufin tattauna shirin dawowa  makarantu bayan hutun da aka yi a jihar.

Ya bayyana cewa, gwamnatin jihar ta sanya bangaren ilimi a sahun gaba saboda muhimmancinsa ga ci gaban jihar.

Kwamishinan ya nuna cewa gwamnatin jihar ta dauki malamai 7,000 domin inganta tsarin koyarwa a makarantu, inda ya kara da cewa za a dauki ma’aikatan girki na J-Cook domin kara karfafa harkar gudanarwar makarantu.

A jawabansu daban-daban, wasu daga cikin Daraktoci da Shugabannin makarantu, sun bukaci a sake duba kudaden gudanar da makarantu, da samar da kwamfutoci da kayan aikinsu, da bayar da tallafi da kuma samar da malamai domin inganta ayyukan koyarwa.

 

Usman Muhammad Zaria 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa

Tun Farko tawagar gwamnatin ta Isa fadar hakimin Barnawa domin isar da sakon ta’aziyyar gwamnatin jihar kaduna na rashin matashi inda suka tabbatar wa da Hakimin cewa gwamnatin jihar kaduna zatayi duk Mai yiwuwa wajen ganin anyiwa matashi Abubakar adalci da kuma gano dalilin mutuwarsa.

 

Hakazalika, tawagar gwamnan sun Kai ziyarar jaje gidan mamacin domin jajantawa iyayensa da ‘yan uwansa .

 

“kwamishinan ya Kara da cewa ‘Mai girma gwamna Uba Sani Yaso yazo da kansa amma bisa wasu abubuwa da suka bijiro hakan ya sanya ya wakilto mu saboda haka gwamna ya kadu matuka da samun labarin rasuwar Abubakar”.

 

Maiyaki, yace domin ganin an dakile matsalar yawaitar tu’ammali da muyagun kwayoyi, gwamnatin jihar Kaduna ta Kafa wani kwamitin hadin gwiwa na jami’an tsaro yaki da masu sha da fataucin muyagun kwayoyi a jihar.

 

Hakazalika, ya bukaci daukacin alummar jihar musamman matasa da su kaucewa tu’ammali da muyagun kwayoyi domin Kara samum zaman lafiya a fadin jihar baki daya.

 

Akan, yayi Kira ga iyaye da matasa da su baiwa jami’an tsaro goyon bayan da suka kamata wajen dakile matsalar shaye-shayen muyagun kwayoyi.

 

Ya kuma jinjinawa kokarin Hakimin Barnawa Alhaji Kabiru Zubairu na Kara hada kan al’umma da wajen tabbatar da zaman lafiya ya Kara sanuwa a garin Barnawa Dama jihar Kaduna baki daya.

 

A nasa jawabin Kwanishinan Ma’aikatar tsaro da harkikin cikin gida na jihar kaduna Barista Suleman Shu’aibu ( SAN) yace zaman lafiya da Samar da tsaro yana daga cikin manyan kudurorin gwamna Uba Sani inda ya bayar da tabbacin cewa zasu ci gaba da duk Mai yiwuwa wajen kare rayuka da dukuyoyin alummar jihar Baki daya.

 

Akan hakan, yayi Kira ga alummar jihar da su ci gaba da baiwa jami’an tsaro goyon bayan da suka kamata wajen ganin an magance matsalar bata gari Wanda hakan zai tqimakawa kokarin gwamnati na kara Samar da ayyukan ci gaba a ciki da wajen jihar.

 

Da yake nasa jawabin hakimin Barnawa kuma Madaucin Arewan Zazzau Alhaji Kabiru Zubairu, yace babu abunda da zasu cewa gwamnatin jihar kaduna sai Fatan alkhairi da samun nasara.

 

Yace alummar Barnawa zasu tabbatar da cewa su ci gaba da marawa gwamnatin Uba Sani baya domin ci gaba da aiwatar da ayyukan da takeyi na ci ga.

 

Anasa jawabin kwamishinan da lamuran cikin gida Barista Suleiman Shu’aibu ( SAN) yace gwamnatin jihar Kaduna bata ji dadin abinda da faru ba inda lamarin ya faru ne bisa kuskure inda Yayi addu’ar Allah ya gafartawa mamacin.

 

A nasa jawabin hakimin Barnawa Alhaji Kabiru Zubairu ( Badauchin Arewan Zazzau) yace tun lokacin da lamarin ya faru jami’an tsaro sun bayar da gudummawa wajen ganin an samu zaman lafiya.

 

‘Wannan yaro da ya rasu jika ne a wurina Saboda ‘ya ta ce ta haife shi saboda haka muna da tabbacin cewa yayi shahada ne. Wannan mataki da gwamnan jihar Kaduna ya dauka na kawo mana gaisuwa bazamu manta da shi saboda ya karrrama mu kwarai da gaske Kuma.

 

Suma iyayen mamacin sun nuna Jin dadinsu da irin matakin da gwamnatin jihar kaduna ta dauka na aiwatar da bincike abin a yaba ne.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kai Ziyarar Gani Da Ido A Karamar Hukumar Gwiwa
  • Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa
  • Akwai Bukatar Samar Da Sauyin Zaman Lafiya Mai Dorewa A Duniya — Maryam Bukar
  • Tetfund Ta Samar Da Naira Biliyan 100 Don Inganta Ilimin Likitanci – Masari
  • Matsalar ƙofa ta hana fasinjoji 58 hawa jirgin Abuja zuwa Landan
  • Cire Tallafin Mai Ya Taimaka Mana Wajen Aiwatar da Ayyuka, In Ji Gwamna Mbah
  • Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Gina Asibitin Dabbobi A Jihar Kwara
  • Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Masana’antar Lantarki Ya Ci Gaba Da Samun Karfin Juriya A Kasar Sin
  • Akwai buƙatar samar da sauyin zaman lafiya mai ɗorewa — Maryam Bukar
  • Jihar Jigawa Za Ta Hada Gwiwa Da Liberia Don Inganta Noman Shinkafa