Shugaban Duruz A Kasar Syria Ya Ki Amincewa Da Sabon Tsarin Mulkin Kasar
Published: 19th, March 2025 GMT
Shugaban na kurdawa a Syira Hikmat al-Hijri ya soki halayyar gwamnatin rikon kwarya ta kasar Syria, tare da nuna kin amincewa da sabon tsarin mulkin kasar da aka sanar kwanaki kadan da su ka gabata.
Hikmata al-Hijri ya yi kira da gyara yadda ake tafiya a yanzu da kuma rubuta sabon tsarin mulki wanda zai zama yana wakiltar dukkanin bangarorin mutanen kasar.
Shugaban na ‘yan Duruz ya bayyana cewa; sabon tsarin mulkin da aka gabatar yana nuni ne da mahangar wani bangare daya na al’ummar kasar, wanda kuma yake share fage na kafa tsarin kama-karya, maimakon kafa tsarin demokradiyya. Haka nan kuma ya ce, ko kadan ba a yi aiki da tsarin da zai kai ga kafa hukuma ba, sannan kuma gwamnatin rikon kwarya ta yi watsi da abinda al’ummar kasar suke son cimmawa ta hanyar juyin da su ka yi.
Dangane da taron kasa da aka yi, shugaban ‘yan Duruz din ya ce, taro ne na sa’o’i 5 kadai wanda kuma ba musayar ra’ayi aka yi ba, an gabatarwa da mahalartarsa umarni ne na abinda ake son yi, don haka gwiwar mutane ta yi sanyi.
Haka nan kuma shugaban na Kurdawa ya zargi kungiyar “Tahrirus-Sham’ da cewa ta damfarawa al’ummar Syria shugabanninta wadanda ba kwararru ba ne, haka nan kuma an kori ma’aikatan gwamnati da dama daga aiki cikin tilasci.
Akan abinda ya faru a gabar ruwan Syria shugaban na ‘yan Duruz ya dorawa gwamnatin alhaki, yana mai yin tuni da cewa, laifukan da aka tafka sun yi kama da wadanda “ Da’esh’ ta aikata.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaba Tinubu Ya Taya Sabon Firaiministan Kanada Mark Carney Murna
Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya Mista Mark Joseph Carney murna bisa zaɓensa a matsayin Firaiminista na 24 na ƙasar Kanada, bayan nasarar jam’iyyar Liberal a zaɓen majalisar dokokin da aka kammala kwanan nan.
A cikin wata sanarwa da mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yada labarai Bayo Onanuga, ya fitar, Shugaba Tinubu ya bayyana zaman Carney a wannan matsayi a matsayin wani muhimmin ci gaba, musamman a wannan lokaci da Kanada ke bukatar gogaggen shugaba domin fuskantar ƙalubale da dama.
Carney, wanda fitaccen masani ne a fannin tattalin arziki, ya taba rike mukamin Gwamnan Babban Bankin Kanada daga shekarar 2008 zuwa 2013, sannan ya ci gaba da zama Gwamnan Babban Bankin Ingila daga 2013 zuwa 2020.
Shugaba Tinubu ya bayyana kwarin gwiwar cewa ƙwarewar sabon shugaban Kanada a fannin kuɗi da shugabanci za ta taka muhimmiyar rawa wajen gina makomar ƙasar. Haka kuma, ya sake jaddada kudirin Najeriya na ƙarfafa dangantakar diflomasiyya da Kanada, musamman a fannonin ilimi, sauyin yanayi da hijira.
Shugaban Najeriya ya ƙara da cewa yana fatan kafa kyakkyawan hadin gwiwa da gwamnatin Carney, yayin da ya nuna godiyarsa ga kyakkyawar alakar da aka kula a tsakaninsu a zamanin tsohon Firayim Minista, Justin Trudeau.
Bello Wakili