Shugaban Duruz A Kasar Syria Ya Ki Amincewa Da Sabon Tsarin Mulkin Kasar
Published: 19th, March 2025 GMT
Shugaban na kurdawa a Syira Hikmat al-Hijri ya soki halayyar gwamnatin rikon kwarya ta kasar Syria, tare da nuna kin amincewa da sabon tsarin mulkin kasar da aka sanar kwanaki kadan da su ka gabata.
Hikmata al-Hijri ya yi kira da gyara yadda ake tafiya a yanzu da kuma rubuta sabon tsarin mulki wanda zai zama yana wakiltar dukkanin bangarorin mutanen kasar.
Shugaban na ‘yan Duruz ya bayyana cewa; sabon tsarin mulkin da aka gabatar yana nuni ne da mahangar wani bangare daya na al’ummar kasar, wanda kuma yake share fage na kafa tsarin kama-karya, maimakon kafa tsarin demokradiyya. Haka nan kuma ya ce, ko kadan ba a yi aiki da tsarin da zai kai ga kafa hukuma ba, sannan kuma gwamnatin rikon kwarya ta yi watsi da abinda al’ummar kasar suke son cimmawa ta hanyar juyin da su ka yi.
Dangane da taron kasa da aka yi, shugaban ‘yan Duruz din ya ce, taro ne na sa’o’i 5 kadai wanda kuma ba musayar ra’ayi aka yi ba, an gabatarwa da mahalartarsa umarni ne na abinda ake son yi, don haka gwiwar mutane ta yi sanyi.
Haka nan kuma shugaban na Kurdawa ya zargi kungiyar “Tahrirus-Sham’ da cewa ta damfarawa al’ummar Syria shugabanninta wadanda ba kwararru ba ne, haka nan kuma an kori ma’aikatan gwamnati da dama daga aiki cikin tilasci.
Akan abinda ya faru a gabar ruwan Syria shugaban na ‘yan Duruz ya dorawa gwamnatin alhaki, yana mai yin tuni da cewa, laifukan da aka tafka sun yi kama da wadanda “ Da’esh’ ta aikata.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
AU ta janye takunkumin da ta ƙaƙaba wa Gabon
Ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU) ta janye takunkuman da ta ƙaƙaba wa Gabon bayan dakatar da ƙasar ta Tsakiyar Afirka saboda juyin mulkin da aka yi a watan Agustan 2023.
Wani taro da aka yi na Kwamitin Zaman Lafiya da Tsaro kan sauyin siyasa a Gabon “ya yi nazari kan ayyukan tare da gano cewa sun yi nasara,” in ji shashen Siyasa da Zaman Lafiya da Tsaro na AU a shafin X a ranar Laraba.
Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta Nijeriya Dalilin da manyan ’yan siyasa ke barin NNPP — APCSanarwar ta ce za a yi maraba da Gabon “ta dawo nan da nan, ta ci gaba da shiga ayyuka” a sakatariyar Tarayyar Afirka.
An dakatar da Gabon a lokacin da Janaral Brice Oligui Nguema ya ƙwace mulki bayan kifar da gwamnatin Shugaba Ali Bongo, wanda iyalinsa suka yi mulki tsawon shekaru 55.
Nguema ya yi alkawarin miƙa mulkin ƙasar mai arzikin man fetur ga farar hula bayan shekaru biyu na riƙon ƙwarya, kuma an zaɓe shi a matsayin shugaban farar hula da kashi 94 na kuri’un da aka kaɗa.
Sabon kundin tsarin mulkin da aka samar ya tanadi cewa shugaban ƙasar zai yi mulkin ƙasar da faffaɗan iko.
Matakin da Tarayyar Afirka ta ɗauka ya biyo bayan taron da aka yi a makon da ya gabata tsakanin Nguema da shugaban Ivory Coast Alassane Ouattara, inda Nguema ya nemi goyon baya ta hanyar janye masa takunkuman.
Kasar mai yawan mutane miliyan 2.3 tana fama da rashin ayyukan yi, da katsewar lantarki da rashin ruwan sha, da basussuka a suka yi wa gwamnati katutu duk da arzikin mai da take da shi.