Shugaban Duruz A Kasar Syria Ya Ki Amincewa Da Sabon Tsarin Mulkin Kasar
Published: 19th, March 2025 GMT
Shugaban na kurdawa a Syira Hikmat al-Hijri ya soki halayyar gwamnatin rikon kwarya ta kasar Syria, tare da nuna kin amincewa da sabon tsarin mulkin kasar da aka sanar kwanaki kadan da su ka gabata.
Hikmata al-Hijri ya yi kira da gyara yadda ake tafiya a yanzu da kuma rubuta sabon tsarin mulki wanda zai zama yana wakiltar dukkanin bangarorin mutanen kasar.
Shugaban na ‘yan Duruz ya bayyana cewa; sabon tsarin mulkin da aka gabatar yana nuni ne da mahangar wani bangare daya na al’ummar kasar, wanda kuma yake share fage na kafa tsarin kama-karya, maimakon kafa tsarin demokradiyya. Haka nan kuma ya ce, ko kadan ba a yi aiki da tsarin da zai kai ga kafa hukuma ba, sannan kuma gwamnatin rikon kwarya ta yi watsi da abinda al’ummar kasar suke son cimmawa ta hanyar juyin da su ka yi.
Dangane da taron kasa da aka yi, shugaban ‘yan Duruz din ya ce, taro ne na sa’o’i 5 kadai wanda kuma ba musayar ra’ayi aka yi ba, an gabatarwa da mahalartarsa umarni ne na abinda ake son yi, don haka gwiwar mutane ta yi sanyi.
Haka nan kuma shugaban na Kurdawa ya zargi kungiyar “Tahrirus-Sham’ da cewa ta damfarawa al’ummar Syria shugabanninta wadanda ba kwararru ba ne, haka nan kuma an kori ma’aikatan gwamnati da dama daga aiki cikin tilasci.
Akan abinda ya faru a gabar ruwan Syria shugaban na ‘yan Duruz ya dorawa gwamnatin alhaki, yana mai yin tuni da cewa, laifukan da aka tafka sun yi kama da wadanda “ Da’esh’ ta aikata.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan sanda sun ƙaddamar da sabon samame, sun kama mutum 98 a Kano
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano, ta kama mutum 98 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban, ciki har da fashi da makami, safarar miyagun ƙwayoyi, sata, zamba da kuma tayar da hankalin jama’a.
An kama waɗannan mutane ne ƙarƙashin sabon samamen da rundunar ta ƙaddamar mai suna “Operation Kukan Kura” wanda ya fara aiki a ranar 1 ga watan Yuli, 2025.
Kotun ƙoli ta tabbatar da Okpebholo a matsayin gwamnan Edo Jami’ar Tarayya ta Gashuwa za ta ba matar Tinubu digirin girmamawaKwamishinan ’Yan Sandan Kano, Ibrahim Adamu Bakori, ne ya bayyana hakan yayin taron manema labarai da aka gudanar a hedikwatar rundunar da ke Bompai a ranar Alhamis.
Ya ce wannan aiki wani ɓangare ne na ƙoƙarin daƙile aikata laifuka da tabbatar da zaman lafiya a faɗin Jihar Kano.
Ya ce samamen ya samu goyon bayan Sufetan Janar na ’Yan Sanda, Kayode Adeolu Egbetokun, domin ƙarfafa haɗin kai da al’umma wajen yaƙi da laifuka.
Kwamishinan, ya bayyana cewa wannan aiki yana bin tsarin aikin rundunar, wanda ke nufin haɗa kai da al’umma wajen hana aikata laifuka.
Rundunar ta nazarci halin tsaro a jihar tare da duba yankunan da laifuka suka fi yawa kafin ta ƙaddamar da samamen.
Ya ce babban burin wannan aiki shi ne zama tamkar wata hanyar gargaɗi domin gano da kuma daƙile barazanar laifuka tun kafin su faru.
Daga cikin waɗanda aka kama akwai mutum 21 da ake zargi da fashi da makami, huɗu ana zargin su da garkuwa da mutane, biyar kan safarar miyagun ƙwayoyi.
Sauran sun haɗa da mutum 12 da ake zargi da satar motoci, huɗu ana zargin su da zamba, sai wasu biyar da ake zargi da sata, da kuma mutum 47 da ake zargi da tayar da hankalin jama’a.
Kayayyakin da aka ƙwato sun haɗa da motoci guda shida, adaidaita sahu guda takwas, babura guda tara, tabar wiwi, kwalabe 86 na kayan maye, takubba 16 da wuƙaƙe.
Kwamishinan, ya ce waɗannan nasarori za a ci gaba da amfani da su wajen inganta dabarun aiki da rundunar ke aiwatarwa.
Ya ƙara da cewa rundunar za ta ci gaba da ɗaukar matakan kare rayuka da dukiyoyin al’ummar Jihar Kano.