‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Published: 19th, March 2025 GMT
Wani mazaunin yankin ya koka da yadda ‘yan bindiga ke yawan kai hare-hare a waɗannan wurare, lamarin da ya sa jama’a ke cikin fargaba.
A Farin-Shinge, mazauna yankin sun nuna koka kan hare-haren da ke ci gaba da faruwa, inda suka roƙi gwamnati da hukumomin tsaro su ɗauki matakin gaggawa.
Kakakin rundunar ‘yansandan Jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da harin kuma ya ce za su binciki lamarin.
Sai dai, har zuwa lokacin da aka haɗa wannan rahoto, ba a samu ƙarin bayani daga ‘yansanda ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
An garzaya da shi zuwa babban Asibitin Gwamnatin Tarayya da ke Birnin Kebbi, inda daga bisani likitoci suka tabbatar da rasuwarsa.
An yi jana’izarsa a babban masallacin Sarkin Gwandu, sannan aka binne shi a makabartar Dukku da ke kan hanyar Makera zuwa Kangiwa.
Jana’izar ta samu halartar jami’an kwas5tan, ‘yan uwa, abokai da sauran mu5sulmi daga sassa daban-daban na jihar.
Har yanzu al’ummar garin Filgila da kewaye na cikin tashin hankali da fargaba, kasancewar hare-haren Lakurawa na jefa su cikin zulumi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp